ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Kasar Sin Da “Wuce Misali” Ba Shi Da Tushe Ko Makama

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Cikin manyan batutuwa da sakatariyar baitil-malin Amurka Janet Yellen ta tabo, yayin ziyarar kwana kwanan nan da ta yi a kasar Sin, akwai zargin Sin da “Wuce Misali” a fannin bunkasa masana’antu masu alaka da makamashi mai tsafta, ciki har da na samar da ababen hawa masu aiki da lantarki.

Kafin ziyarar Yellen, kafafen watsa labaran Amurka sun yi ta yayata batun nan na “Wuce Misali” a fannin kere keren kasar Sin, suna zargin Sin din da cika kasuwannin duniya da kayayyakin fitarwa ketare masu rahusa, irin su farantan samar da lantarki ta hasken rana da ababen hawa masu aiki da lantarki.

  • Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Shugaban Kasar Mozambique
  • Firaministan Kasar Sin Ya Jagoranci Taron Neman Ra’ayi Kan Aikin Tattalin Arziki

To sai dai kuma, wadannan zarge-zarge ba su da tushe ko makama. Suna kuma fayyacewa duniya halayyar masu tsara manufofi na Amurka, dake da tunanin ko kasar su ta samu, ko kuma kowa ya rasa.

ADVERTISEMENT

Karkashin irin wannan tunani ne mahukuntan Amurka suka kakaba takunkumin hana fitar da sassan laturori na kamfanonin kasar zuwa kasuwannin Sin, da hana wasu kamfanonin Sin din damar kasuwanci na halak ta fakewa da tsaron kasa.

Har ila yau, irin wadannan matakai na nuni ga matsayin Amurka na aiwatar da manufofi idan kawai za su yi daidai da moriyar kasar, da saba musu idan za su amfani sauran sassa. Wato dai a duk lokacin da masana’antun Amurka za su ci wata gajiya, kasar na yin “Uwa da makarbiya” wajen ganin sun cimma nasara, amma idan kamfanonin kasar za su yi takara da na sauran sassan duniya, sai Amurkan ta sanya shinge na baiwa kamfanoninta kariya, wanda hakan sam ya sabawa adalci.

LABARAI MASU NASABA

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

A gani na, maimakon zargin “Wuce Misali” kan kamfanoni masu alaka da makamashi mai tsafta na Sin, kamata ya yi ma Amurka da sauran kasashen duniya su goyi bayan ci gaban wannan fasahohi, duba da cewa a yanzu haka ana kan wata gaba da kasashen duniya ke ta kokarin sauya alkibla zuwa amfani da nau’o’in makamashi marasa gurbatawa da dumama yanayi.

A daya bangaren kuma, mun san cewa Sin da Amurka kasashe ne dake da bangarori da dama na hadin gwiwa da cin moriyar juna. Don haka ne ma har kullum, mahukuntan kasar Sin ke ganin abun da ya fi dacewa shi ne sassan biyu su ingiza ci gaban juna maimakon takawa juna birki, a dukkanin bangarori na ci gaba da aka saba da su na cinikayya, da noma, da ma sabbin fannoni irin su na kare yanayi, da fasahohi, da ayyukan kirkirarriyar basira ko AI.

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

MASU ALAKA

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin
Daga Birnin Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Yiwu Ta Duniya –Yadda Xi Jinping Ke Kulawa Da Jagorantar Ci Gaban Yiwu”

July 25, 2026
Next Post
Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Afirka Ya Samu Bunkasuwa A 2023

Jarin Kai Tsaye Da Sin Ta Zuba A Afirka Ya Samu Bunkasuwa A 2023

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Sin

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026
Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

Arewa Ta Rasa Alƙiblarta – Dattawan Arewa

July 26, 2026
Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

Dauda Dauda Lawal Ya Sha Alwashin Farfaɗo Da Masana’antar Yadi Ta Zamfara

July 26, 2026
Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000  A Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

July 26, 2026
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Birtaniya Ta Yaba Wa Tinubu Kan Sauye-sauyen Tattalin Arziki

July 25, 2026
Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

Ofishin Jakadancin Sin A Nijeriya Ya Shirya Taron Murnar Cika Shekaru 99 Da Kafuwar Rundunar PLA Ta Sin

July 25, 2026
Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

Farfesa Dr. Otto Heinrich Herzog: Sin Tana Da Tsari Mai Kyau Na Aiwatar Da Dabarun Ci Gaba

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.