• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Luwaɗi Da Maɗigo: Gwamnatin Bauchi Ta Gayyaci Sheikh Gadon-Kaya Don Ƙarin Haske

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
1 year ago
Madigo

Gwamnatin jihar Bauchi ta aike da saƙon gayyata kai tsaye ga fitaccen malamin addinin musulunci da ke jihar Kano, Dakta Abdallah Gadon-Ƙaya domin yi mata ƙarin haske kan jawabin da ya yi da ke cewa, akwai wasu masu shirya luwaɗi da maɗigo a wani otel da ke jihar Bauchi.

 

Shi dai Dakta Gadon-Ƙaya ya fito a wani faifan bidiyo inda ya ke sanar da duniya cewa, wani ya kirasa a waya ya shaida masa cewa, akwai wani otel da aka ɗauki hayarsa na tsawon kwanaki da kuɗi da ya kai miliyan 100 domin yin maɗigo da luwaɗi da auren jinsi a jihar Bauchi, inda ya ce, masu aikata hakan sun fito ne daga jihohi daban-daban domin sheƙe ayarsu. Har ma ya ce idan ana buƙata zai bada sunan otel ɗin.

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Takwas A Karamar Hukumar Birnin Gwari Ta Kaduna
  • Tinubu Zai Kai Ziyara Kasar Sin Domin Haɓaka Tattalin Arziki  Da Kayayyakin More Rayuwa 

A ganawarsa da ‘yan jarida, shugaban hukumar Shari’a ta jihar Bauchi, Farfesa Hamisu Dass, ya ce, gayyatar ta zama dole lura da girman abun da ake zargin wasu na aikatawa a jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

“Tun bayan jin jawabin na babban malamin, hankalin mai girma gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed da Kwamishinan harkokin addinai da mu kanmu hankulanmu sun tashi. Jihar Bauchi, jiha ce da kowa yasan ba za ta amince da nau’ikan wannan rashin ɗa’ar ba, kowa ya san irin ƙoƙarin da gwamnan ke yi wajen kyautata tarbiyya da ɗa’a a tsakanin jama’a.

 

“Don haka, jin wannan bayanin ya tada mana hankali sosai. A bisa wannan, mun gayyaci jami’an hotel ɗin da ake zargi da cewa wannan abun ya faru ciki, kuma shi ma malamin mun aika masa da gayyata domin mu gano haƙiƙanin abun da ya faru”

 

Shugaban ya ce, tunin suka ƙaddamar da bincike da sanya ido a otel ɗin da ma sauran otel da suke jihar domin daƙile dukkanin wani lamari da ya shafi irin wannan.

 

Sai dai ya nuna takaici kan yadda malamin ya hau lasifika ya kama bayyana irin wannan babban lamarin ba tare da ya ankarar da gwamnatin jihar ba, “Irin wannan zai sanya masu laifin ma su gudu ko su ɓuya. Amma da an sanar mana nan take za mu ɗauki matakin gaggawa.”

 

Farfesa Dass ya nemi al’umma da su kwantar da hankalinsu inda ya ce, tuni aka ƙaddamar da bincike kuma tabbas in akwai wani batu makamancin wannan to za su ɗauki matakin dakile shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma
Labarai

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
tinubu
Labarai

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Next Post
Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Karfafa Kawance Da Bunkasa Damammakin Hadin Gwiwa

Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Karfafa Kawance Da Bunkasa Damammakin Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.