ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Luwaɗi Da Maɗigo: Gwamnatin Bauchi Ta Gayyaci Sheikh Gadon-Kaya Don Ƙarin Haske

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 years ago
Madigo

Gwamnatin jihar Bauchi ta aike da saƙon gayyata kai tsaye ga fitaccen malamin addinin musulunci da ke jihar Kano, Dakta Abdallah Gadon-Ƙaya domin yi mata ƙarin haske kan jawabin da ya yi da ke cewa, akwai wasu masu shirya luwaɗi da maɗigo a wani otel da ke jihar Bauchi.

 

Shi dai Dakta Gadon-Ƙaya ya fito a wani faifan bidiyo inda ya ke sanar da duniya cewa, wani ya kirasa a waya ya shaida masa cewa, akwai wani otel da aka ɗauki hayarsa na tsawon kwanaki da kuɗi da ya kai miliyan 100 domin yin maɗigo da luwaɗi da auren jinsi a jihar Bauchi, inda ya ce, masu aikata hakan sun fito ne daga jihohi daban-daban domin sheƙe ayarsu. Har ma ya ce idan ana buƙata zai bada sunan otel ɗin.

ADVERTISEMENT
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Takwas A Karamar Hukumar Birnin Gwari Ta Kaduna
  • Tinubu Zai Kai Ziyara Kasar Sin Domin Haɓaka Tattalin Arziki  Da Kayayyakin More Rayuwa 

A ganawarsa da ‘yan jarida, shugaban hukumar Shari’a ta jihar Bauchi, Farfesa Hamisu Dass, ya ce, gayyatar ta zama dole lura da girman abun da ake zargin wasu na aikatawa a jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Tun bayan jin jawabin na babban malamin, hankalin mai girma gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed da Kwamishinan harkokin addinai da mu kanmu hankulanmu sun tashi. Jihar Bauchi, jiha ce da kowa yasan ba za ta amince da nau’ikan wannan rashin ɗa’ar ba, kowa ya san irin ƙoƙarin da gwamnan ke yi wajen kyautata tarbiyya da ɗa’a a tsakanin jama’a.

 

“Don haka, jin wannan bayanin ya tada mana hankali sosai. A bisa wannan, mun gayyaci jami’an hotel ɗin da ake zargi da cewa wannan abun ya faru ciki, kuma shi ma malamin mun aika masa da gayyata domin mu gano haƙiƙanin abun da ya faru”

 

Shugaban ya ce, tunin suka ƙaddamar da bincike da sanya ido a otel ɗin da ma sauran otel da suke jihar domin daƙile dukkanin wani lamari da ya shafi irin wannan.

 

Sai dai ya nuna takaici kan yadda malamin ya hau lasifika ya kama bayyana irin wannan babban lamarin ba tare da ya ankarar da gwamnatin jihar ba, “Irin wannan zai sanya masu laifin ma su gudu ko su ɓuya. Amma da an sanar mana nan take za mu ɗauki matakin gaggawa.”

 

Farfesa Dass ya nemi al’umma da su kwantar da hankalinsu inda ya ce, tuni aka ƙaddamar da bincike kuma tabbas in akwai wani batu makamancin wannan to za su ɗauki matakin dakile shi.

Madigo
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba
Madigo
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Karfafa Kawance Da Bunkasa Damammakin Hadin Gwiwa

Sin Da Kasashen Afirka Na Kara Karfafa Kawance Da Bunkasa Damammakin Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.