• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Tarkon Bashi Ba Zai Katse Alakar Sin Da Kasashen Afirka Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Zargin Tarkon Bashi Ba Zai Katse Alakar Sin Da Kasashen Afirka Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sau da yawa mun sha jin yadda wasu kasashen yammacin duniya, da kafofin watsa labaransu na furta kalamai na zargi, cewa wai kasar Sin tana danawa kasashen dake nahiyar Afirka Tarko Bashi, karkashin manufofinta na cudanyar da kasashe masu tasowa.

Irin wadannan sassan, kan Ambato shawarar ziri daya da hanya daya, a matsayin shiri dake dorawa kasashen na Afirka tarin bashi da ba za su iya biya ba. To amma abun tambayar shi ne, ko kasashen na Afirka suna da irin wannan tunani?

  • Jarin Waje Da Sin Ta Yi Amfani A Zahiri Ya Karu A Shekarar 2022

A zahiri dai, ba wata kafa da ta taba fito da shaidu, ko kafa sahihan dalilai kan wancan zargi da wasu kasashen yamma ke yiwa kasar Sin. Hasali ma, sau da yawa mun sha jin shugabannin kasashen Afirka na godewa irin tallafi, da gudummawar da Sin din ke ba su, a kokarinsu na raya kasa da samun ci gaba mai dorewa.

Ko da a yayin ziyarar aiki da ministan harkokin wajen kasar Sin Qing Gang ya kai kasashen Afirka 5, da helkwatar AU, da kungiyar tarayyar Larabawa a baya bayan nan, mun ga irin yadda bangarorin da ya zanta da su suka rika nuna gamsuwa, da godiya kan manufofin kasar Sin, na tafiya tare da kawayenta na Afirka, a matsayinsu na aminai, kuma ’yan uwan ta kasashe masu tasowa.

Kaza lika, masana tattalin arziki da dama na bayyana cewa, bashin da gwamnatoci ke karba daga waje, ba ya haifar da koma bayan tattalin arziki, muddin an aiwatar da sharudda, da matakan cin gajiyarsa yadda ya kamata. Kuma karkashin hakan ne ragowar cibiyoyin bayar da lamuni na yammacin duniya, suke baiwa kasashen na Afirka lamuni mai kudin ruwa, tare da gindaya sharudda gare su na biyan basussukan. Sabanin haka, kasar Sin a nata bangare, ba ta gindaya sharudda ga kasashen da take baiwa bashi, kuma bashin Sin yana da rangwame matuka, idan an kwatanta da na sauran cibiyoyin ba da lamuni na kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Idan kuma muka komawa misalai daga su kansu jagororin kasashen Afirka, da kuma alkaluman da hukumomin nahiyar ke fitarwa, game da tasirin lamunin kasar Sin a nahiyar Afirka, za mu ga a kasashe irin su Najeriya, da Zambia, da Kenya da Angola da sauransu, ayyukan more rayuwa da kasar Sin ta tallafawa wajen samarwa, suna zamewa kasashen abubuwan alfahari.

Duba da haka, masharhanta da dama ke cewa, su kansu kasashen yamma, da masana na kasashen yammacin duniya, sun gamsu da kyakkyawan tasirin alakar Sin da kasashen Afirka, da ma yadda Sin din ke samar da tallafi ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewar alummun nahiyar. Amma duk da haka, wasu bangarori na kitsa karairayi, domin bata wannan kyakkyawar alaka, ta fakewa ba batun “Tarkon bashi “. Suna kuma yada kalamai marasa hujja, da nufin siyasantar da alakar dake tsakanin sassan biyu.

Sai dai duk da haka, alamu na zahiri sun tabbatar da cewa, Sin da kasashen Afirka sun amince da juna, kuma ba wani rukuni, ko wasu masu kitsa karairayi da za su iya yin nasarar bata wannan kyakkyawar alakar da sassan biyu suka gina cikin tsawon lokaci. (Saminu Hassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Zai Hukunta Bankuna Da Ba Su Fara Bayar Da Sabbin Takardun Kudi Ba

Next Post

Na Sake Dawowa Musulunci, Cewar JJC Skills

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

19 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

20 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

21 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

22 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

23 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

2 days ago
Next Post
Na Sake Dawowa Musulunci, Cewar JJC Skills

Na Sake Dawowa Musulunci, Cewar JJC Skills

LABARAI MASU NASABA

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.