• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Tarkon Bashi Ba Zai Katse Alakar Sin Da Kasashen Afirka Ba

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Zargin Tarkon Bashi Ba Zai Katse Alakar Sin Da Kasashen Afirka Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sau da yawa mun sha jin yadda wasu kasashen yammacin duniya, da kafofin watsa labaransu na furta kalamai na zargi, cewa wai kasar Sin tana danawa kasashen dake nahiyar Afirka Tarko Bashi, karkashin manufofinta na cudanyar da kasashe masu tasowa.

Irin wadannan sassan, kan Ambato shawarar ziri daya da hanya daya, a matsayin shiri dake dorawa kasashen na Afirka tarin bashi da ba za su iya biya ba. To amma abun tambayar shi ne, ko kasashen na Afirka suna da irin wannan tunani?

  • Jarin Waje Da Sin Ta Yi Amfani A Zahiri Ya Karu A Shekarar 2022

A zahiri dai, ba wata kafa da ta taba fito da shaidu, ko kafa sahihan dalilai kan wancan zargi da wasu kasashen yamma ke yiwa kasar Sin. Hasali ma, sau da yawa mun sha jin shugabannin kasashen Afirka na godewa irin tallafi, da gudummawar da Sin din ke ba su, a kokarinsu na raya kasa da samun ci gaba mai dorewa.

Ko da a yayin ziyarar aiki da ministan harkokin wajen kasar Sin Qing Gang ya kai kasashen Afirka 5, da helkwatar AU, da kungiyar tarayyar Larabawa a baya bayan nan, mun ga irin yadda bangarorin da ya zanta da su suka rika nuna gamsuwa, da godiya kan manufofin kasar Sin, na tafiya tare da kawayenta na Afirka, a matsayinsu na aminai, kuma ’yan uwan ta kasashe masu tasowa.

Kaza lika, masana tattalin arziki da dama na bayyana cewa, bashin da gwamnatoci ke karba daga waje, ba ya haifar da koma bayan tattalin arziki, muddin an aiwatar da sharudda, da matakan cin gajiyarsa yadda ya kamata. Kuma karkashin hakan ne ragowar cibiyoyin bayar da lamuni na yammacin duniya, suke baiwa kasashen na Afirka lamuni mai kudin ruwa, tare da gindaya sharudda gare su na biyan basussukan. Sabanin haka, kasar Sin a nata bangare, ba ta gindaya sharudda ga kasashen da take baiwa bashi, kuma bashin Sin yana da rangwame matuka, idan an kwatanta da na sauran cibiyoyin ba da lamuni na kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Idan kuma muka komawa misalai daga su kansu jagororin kasashen Afirka, da kuma alkaluman da hukumomin nahiyar ke fitarwa, game da tasirin lamunin kasar Sin a nahiyar Afirka, za mu ga a kasashe irin su Najeriya, da Zambia, da Kenya da Angola da sauransu, ayyukan more rayuwa da kasar Sin ta tallafawa wajen samarwa, suna zamewa kasashen abubuwan alfahari.

Duba da haka, masharhanta da dama ke cewa, su kansu kasashen yamma, da masana na kasashen yammacin duniya, sun gamsu da kyakkyawan tasirin alakar Sin da kasashen Afirka, da ma yadda Sin din ke samar da tallafi ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewar alummun nahiyar. Amma duk da haka, wasu bangarori na kitsa karairayi, domin bata wannan kyakkyawar alaka, ta fakewa ba batun “Tarkon bashi “. Suna kuma yada kalamai marasa hujja, da nufin siyasantar da alakar dake tsakanin sassan biyu.

Sai dai duk da haka, alamu na zahiri sun tabbatar da cewa, Sin da kasashen Afirka sun amince da juna, kuma ba wani rukuni, ko wasu masu kitsa karairayi da za su iya yin nasarar bata wannan kyakkyawar alakar da sassan biyu suka gina cikin tsawon lokaci. (Saminu Hassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Zai Hukunta Bankuna Da Ba Su Fara Bayar Da Sabbin Takardun Kudi Ba

Next Post

Na Sake Dawowa Musulunci, Cewar JJC Skills

Related

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

4 hours ago
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
Daga Birnin Sin

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

5 hours ago
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

6 hours ago
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing
Daga Birnin Sin

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

7 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

1 day ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

1 day ago
Next Post
Na Sake Dawowa Musulunci, Cewar JJC Skills

Na Sake Dawowa Musulunci, Cewar JJC Skills

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.