• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zargin Tarkon Bashi Ba Zai Katse Alakar Sin Da Kasashen Afirka Ba

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Zargin Tarkon Bashi Ba Zai Katse Alakar Sin Da Kasashen Afirka Ba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sau da yawa mun sha jin yadda wasu kasashen yammacin duniya, da kafofin watsa labaransu na furta kalamai na zargi, cewa wai kasar Sin tana danawa kasashen dake nahiyar Afirka Tarko Bashi, karkashin manufofinta na cudanyar da kasashe masu tasowa.

Irin wadannan sassan, kan Ambato shawarar ziri daya da hanya daya, a matsayin shiri dake dorawa kasashen na Afirka tarin bashi da ba za su iya biya ba. To amma abun tambayar shi ne, ko kasashen na Afirka suna da irin wannan tunani?

  • Jarin Waje Da Sin Ta Yi Amfani A Zahiri Ya Karu A Shekarar 2022

A zahiri dai, ba wata kafa da ta taba fito da shaidu, ko kafa sahihan dalilai kan wancan zargi da wasu kasashen yamma ke yiwa kasar Sin. Hasali ma, sau da yawa mun sha jin shugabannin kasashen Afirka na godewa irin tallafi, da gudummawar da Sin din ke ba su, a kokarinsu na raya kasa da samun ci gaba mai dorewa.

Ko da a yayin ziyarar aiki da ministan harkokin wajen kasar Sin Qing Gang ya kai kasashen Afirka 5, da helkwatar AU, da kungiyar tarayyar Larabawa a baya bayan nan, mun ga irin yadda bangarorin da ya zanta da su suka rika nuna gamsuwa, da godiya kan manufofin kasar Sin, na tafiya tare da kawayenta na Afirka, a matsayinsu na aminai, kuma ’yan uwan ta kasashe masu tasowa.

Kaza lika, masana tattalin arziki da dama na bayyana cewa, bashin da gwamnatoci ke karba daga waje, ba ya haifar da koma bayan tattalin arziki, muddin an aiwatar da sharudda, da matakan cin gajiyarsa yadda ya kamata. Kuma karkashin hakan ne ragowar cibiyoyin bayar da lamuni na yammacin duniya, suke baiwa kasashen na Afirka lamuni mai kudin ruwa, tare da gindaya sharudda gare su na biyan basussukan. Sabanin haka, kasar Sin a nata bangare, ba ta gindaya sharudda ga kasashen da take baiwa bashi, kuma bashin Sin yana da rangwame matuka, idan an kwatanta da na sauran cibiyoyin ba da lamuni na kasa da kasa.

Labarai Masu Nasaba

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Idan kuma muka komawa misalai daga su kansu jagororin kasashen Afirka, da kuma alkaluman da hukumomin nahiyar ke fitarwa, game da tasirin lamunin kasar Sin a nahiyar Afirka, za mu ga a kasashe irin su Najeriya, da Zambia, da Kenya da Angola da sauransu, ayyukan more rayuwa da kasar Sin ta tallafawa wajen samarwa, suna zamewa kasashen abubuwan alfahari.

Duba da haka, masharhanta da dama ke cewa, su kansu kasashen yamma, da masana na kasashen yammacin duniya, sun gamsu da kyakkyawan tasirin alakar Sin da kasashen Afirka, da ma yadda Sin din ke samar da tallafi ga ci gaban tattalin arziki da zamantakewar alummun nahiyar. Amma duk da haka, wasu bangarori na kitsa karairayi, domin bata wannan kyakkyawar alaka, ta fakewa ba batun “Tarkon bashi “. Suna kuma yada kalamai marasa hujja, da nufin siyasantar da alakar dake tsakanin sassan biyu.

Sai dai duk da haka, alamu na zahiri sun tabbatar da cewa, Sin da kasashen Afirka sun amince da juna, kuma ba wani rukuni, ko wasu masu kitsa karairayi da za su iya yin nasarar bata wannan kyakkyawar alakar da sassan biyu suka gina cikin tsawon lokaci. (Saminu Hassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

CBN Zai Hukunta Bankuna Da Ba Su Fara Bayar Da Sabbin Takardun Kudi Ba

Next Post

Na Sake Dawowa Musulunci, Cewar JJC Skills

Related

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

6 hours ago
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

7 hours ago
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

8 hours ago
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma
Daga Birnin Sin

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

9 hours ago
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5
Daga Birnin Sin

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

10 hours ago
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

11 hours ago
Next Post
Na Sake Dawowa Musulunci, Cewar JJC Skills

Na Sake Dawowa Musulunci, Cewar JJC Skills

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.