• English
  • Business News
Wednesday, October 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zhang Jun: Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Rawar Gani Wajen Cimma Burin Bunkasa Afirka Cikin Lumana

by CGTN Hausa
2 years ago
Zhang Jun

Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Zhang Jun ya ce, kasarsa za ta ci gaba da taka rawar gani, a fannin ingiza bunkasar nahiyar Afirka cikin lumana, tare da fadada hadin gwiwar nahiyar da sauran sassan kasa da kasa.

Zhang, wanda ya bayyana hakan a jiya Alhamis, ya kuma yi amfani da zaman taron kwamitin tsaron MDD da ya gudana a ranar, mai taken “Hadin gwiwa tsakanin MDD da kungiyar AU” wajen bayyana cewa, a shekarun baya bayan nan, kungiyar AU da sauran hukumomin yankin Afirka, na aiki tukuru wajen tunkarar kalubalen zaman lafiya da tsaro, suna kuma kokarin ingiza matakan warware matsalolin nahiyar.

  • Kudaden Da Sin Ta Samarwa Kasashen Afirka Ba Su Kai 10% Na Bashinsu Ba
  • Xi Ya Yi Kira Ga Jiangxi Da Ya Rubuta Nasa Babin A Kokarin Zamanantar Da Kasar Sin

Ya ce yayin da ake tunkarar kalubale daban daban a sassan duniya da yankuna, kamata ya yi kwamitin tsaron MDD ya ci gaba da tallafawa AU, wajen karfafa wannan yunkuri. Kaza lika ya dace tawagogin wanzar da zaman lafiya na MDD su rungumi dabarun da AU ke amfani da su, kana su amince da sauye-sauyen yanayin da ake ciki, su kuma sauke nauyin dake wuyan su yadda ya kamata.

Zhang Jun ya kara da cewa, a halin da ake ciki, yankin kahon Afirka na fuskantar manyan matsaloli masu sarkakiyar warwarewa, kana ana fama da yanayin rashin tabbas a siyasar kasashen yammacin Afirka da Sahel, ga kuma kalubalen ’yan ta’adda dake haifar da tashin hankula, a babban yankin tafkin Chadi. Ya ce wadannan batutuwa ne masu matukar haifar da damuwa. Don haka ya dace MDD ta tallafawa nahiyar Afirka, wajen cimma nasarar muradun dake kunshe cikin ajandar wanzar da ci gaba mai dorewa ta nan da shekarar 2030, kana ta kara azama wajen tallafawa yaki da talauci, da tabbatar da samuwar isasshen abinci, da karfafa samar da muhimman ababen more rayuwa, da fadada samar da guraben ayyukan yi.

Daga nan sai Zhang Jun ya jaddada matsayar kasar Sin, ta mara baya ga sanin makamar aiki tsakanin kasashen nahiyar Afirka, a matsayin daya daga muhimman ginshikai na hadin gwiwa da nahiyar, baya ga burin da Sin din ke da shi na taimakawa nahiyar a fannin bunkasa masana’antu, da zamanantarwa, da wanzar da ci gaba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 
Daga Birnin Sin

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba
Daga Birnin Sin

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Yi Aiki Tare Don Hana Kara Fadada Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Yi Aiki Tare Don Hana Kara Fadada Rikicin Falasdinu Da Isra'ila

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

October 21, 2025
Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

Sin Ta Kammala Ginin Cibiyar Adana Bayanai Mai Amfani Da Karfin Iska A Karkashin Ruwa

October 21, 2025
Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

Aikin Jinya Kyauta: Gwamnatin Zamfara Ta Kammala Zagaye Na 10 Na Kula Da Marasa Lafiya 3,447

October 21, 2025
Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

Ci Gaban Kasar Sin Ya Shaida Cewa Yawan Jama’a Ba Dalili Ne Na Rashin Ci Gaba Ba

October 21, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Gwamna Yusuf Ya Buƙaci Hukumar NBC Da Ta Sa Ido Kan Gidajen Rediyo Da Talabijin Na Yanar Gizo

October 21, 2025
Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

Me Aka Gano Kan Makomar Tattalin Arzikin Kasar Sin Daga Karuwar 5.2% Na Tattalin Arzikinta?

October 21, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Tabbatar Da Yusuf A Matsayin Sabon Shugaban NPC, Wasu 2 A Matsayin Kwamishinoni

October 21, 2025
Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

Jirgin Kasa Mafi Saurin Gudu A Duniya Ya Fara Zirga-Zirgar Gwaji A Sin

October 21, 2025
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

Ma’aikatan Manyan Makarantu Na Kaduna Sun Dakatar Da Yajin Aiki Yayin Da Gwamna Sani Ya Amince Da Sabon Tsarin Albashi

October 21, 2025
Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia

October 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.