ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zhang Jun: Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Rawar Gani Wajen Cimma Burin Bunkasa Afirka Cikin Lumana

by CGTN Hausa
3 years ago
Zhang Jun

Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Zhang Jun ya ce, kasarsa za ta ci gaba da taka rawar gani, a fannin ingiza bunkasar nahiyar Afirka cikin lumana, tare da fadada hadin gwiwar nahiyar da sauran sassan kasa da kasa.

Zhang, wanda ya bayyana hakan a jiya Alhamis, ya kuma yi amfani da zaman taron kwamitin tsaron MDD da ya gudana a ranar, mai taken “Hadin gwiwa tsakanin MDD da kungiyar AU” wajen bayyana cewa, a shekarun baya bayan nan, kungiyar AU da sauran hukumomin yankin Afirka, na aiki tukuru wajen tunkarar kalubalen zaman lafiya da tsaro, suna kuma kokarin ingiza matakan warware matsalolin nahiyar.

  • Kudaden Da Sin Ta Samarwa Kasashen Afirka Ba Su Kai 10% Na Bashinsu Ba
  • Xi Ya Yi Kira Ga Jiangxi Da Ya Rubuta Nasa Babin A Kokarin Zamanantar Da Kasar Sin

Ya ce yayin da ake tunkarar kalubale daban daban a sassan duniya da yankuna, kamata ya yi kwamitin tsaron MDD ya ci gaba da tallafawa AU, wajen karfafa wannan yunkuri. Kaza lika ya dace tawagogin wanzar da zaman lafiya na MDD su rungumi dabarun da AU ke amfani da su, kana su amince da sauye-sauyen yanayin da ake ciki, su kuma sauke nauyin dake wuyan su yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

Zhang Jun ya kara da cewa, a halin da ake ciki, yankin kahon Afirka na fuskantar manyan matsaloli masu sarkakiyar warwarewa, kana ana fama da yanayin rashin tabbas a siyasar kasashen yammacin Afirka da Sahel, ga kuma kalubalen ’yan ta’adda dake haifar da tashin hankula, a babban yankin tafkin Chadi. Ya ce wadannan batutuwa ne masu matukar haifar da damuwa. Don haka ya dace MDD ta tallafawa nahiyar Afirka, wajen cimma nasarar muradun dake kunshe cikin ajandar wanzar da ci gaba mai dorewa ta nan da shekarar 2030, kana ta kara azama wajen tallafawa yaki da talauci, da tabbatar da samuwar isasshen abinci, da karfafa samar da muhimman ababen more rayuwa, da fadada samar da guraben ayyukan yi.

Daga nan sai Zhang Jun ya jaddada matsayar kasar Sin, ta mara baya ga sanin makamar aiki tsakanin kasashen nahiyar Afirka, a matsayin daya daga muhimman ginshikai na hadin gwiwa da nahiyar, baya ga burin da Sin din ke da shi na taimakawa nahiyar a fannin bunkasa masana’antu, da zamanantarwa, da wanzar da ci gaba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Zhang Jun
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

MASU ALAKA

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan
Daga Birnin Sin

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar
Daga Birnin Sin

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Yi Aiki Tare Don Hana Kara Fadada Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Yi Aiki Tare Don Hana Kara Fadada Rikicin Falasdinu Da Isra'ila

LABARAI MASU NASABA

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata

July 5, 2026
Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

Ba Mu Yarda Da Maƙiyanmu Ba, A Shirye Muke —Iran

July 5, 2026
Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

Gasar Kofin Duniya: Ko Morocco Na Iya Tsallake Tarkon Faransa?

July 5, 2026
LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

LeBron James Zai Bar Los Angeles Lakers 

July 5, 2026
Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana

July 5, 2026
Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

Dakarun Tsaron Teku Na Sin Na Ci Gaba Da Sintirin Wanzar Da Doka A Yankunan Ruwa Na Gabashin Tsibirin Taiwan

July 4, 2026
Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

Wasu Matasa Amurkawa Sun Ziyarci Sin Don Kara Fahimtar Kasar

July 4, 2026
Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.