ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zhang Jun: Sin Za Ta Ci Gaba Da Taka Rawar Gani Wajen Cimma Burin Bunkasa Afirka Cikin Lumana

by CGTN Hausa
3 years ago
Zhang Jun

Wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Zhang Jun ya ce, kasarsa za ta ci gaba da taka rawar gani, a fannin ingiza bunkasar nahiyar Afirka cikin lumana, tare da fadada hadin gwiwar nahiyar da sauran sassan kasa da kasa.

Zhang, wanda ya bayyana hakan a jiya Alhamis, ya kuma yi amfani da zaman taron kwamitin tsaron MDD da ya gudana a ranar, mai taken “Hadin gwiwa tsakanin MDD da kungiyar AU” wajen bayyana cewa, a shekarun baya bayan nan, kungiyar AU da sauran hukumomin yankin Afirka, na aiki tukuru wajen tunkarar kalubalen zaman lafiya da tsaro, suna kuma kokarin ingiza matakan warware matsalolin nahiyar.

  • Kudaden Da Sin Ta Samarwa Kasashen Afirka Ba Su Kai 10% Na Bashinsu Ba
  • Xi Ya Yi Kira Ga Jiangxi Da Ya Rubuta Nasa Babin A Kokarin Zamanantar Da Kasar Sin

Ya ce yayin da ake tunkarar kalubale daban daban a sassan duniya da yankuna, kamata ya yi kwamitin tsaron MDD ya ci gaba da tallafawa AU, wajen karfafa wannan yunkuri. Kaza lika ya dace tawagogin wanzar da zaman lafiya na MDD su rungumi dabarun da AU ke amfani da su, kana su amince da sauye-sauyen yanayin da ake ciki, su kuma sauke nauyin dake wuyan su yadda ya kamata.

ADVERTISEMENT

Zhang Jun ya kara da cewa, a halin da ake ciki, yankin kahon Afirka na fuskantar manyan matsaloli masu sarkakiyar warwarewa, kana ana fama da yanayin rashin tabbas a siyasar kasashen yammacin Afirka da Sahel, ga kuma kalubalen ’yan ta’adda dake haifar da tashin hankula, a babban yankin tafkin Chadi. Ya ce wadannan batutuwa ne masu matukar haifar da damuwa. Don haka ya dace MDD ta tallafawa nahiyar Afirka, wajen cimma nasarar muradun dake kunshe cikin ajandar wanzar da ci gaba mai dorewa ta nan da shekarar 2030, kana ta kara azama wajen tallafawa yaki da talauci, da tabbatar da samuwar isasshen abinci, da karfafa samar da muhimman ababen more rayuwa, da fadada samar da guraben ayyukan yi.

Daga nan sai Zhang Jun ya jaddada matsayar kasar Sin, ta mara baya ga sanin makamar aiki tsakanin kasashen nahiyar Afirka, a matsayin daya daga muhimman ginshikai na hadin gwiwa da nahiyar, baya ga burin da Sin din ke da shi na taimakawa nahiyar a fannin bunkasa masana’antu, da zamanantarwa, da wanzar da ci gaba. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Zhang Jun
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

MASU ALAKA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal
Daga Birnin Sin

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba
Daga Birnin Sin

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
Daga Birnin Sin

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Yi Aiki Tare Don Hana Kara Fadada Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Da Su Yi Aiki Tare Don Hana Kara Fadada Rikicin Falasdinu Da Isra'ila

LABARAI MASU NASABA

Zhang Jun

Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP

July 25, 2026
Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

Idan Aka Cire Bangaren Man Fetur Kannywood Ce Ta Fi Samar Da Aikin Yi Ga Matasa —Hamisu Iyantama

July 25, 2026
Kogin Kumadugu Ya Yi Ambaliya Karon Farko Cikin Shekara 100 A Yobe

Jihohi 28 Da Abuja Na Fuskantar Hadarin Ambaliyar Ruwa —Rahoto

July 25, 2026
Zhang Jun

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
Zhang Jun

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.