• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Likitoci Sinawa A Saliyo Za Ta Ceci Rayukan Dimbin Mata

by CMG Hausa
2 years ago
Likitoci Sinawa

Birnin Freetown na Saliyo ya karbi manyan baki a jiya Litinin, wato tawagar likitocin kasar Sin, da za su taimakawa kasar yaki da cutar sankarar bakin mahaifa. 

Sankarar bakin mahaifa, cuta ce da ta zama abar tsoro a tsakanin mata la’akari da yadda take wahalar da su da kai wa ga asarar rai a karshe. A cewar hukumar lafiya ta duniya, a shekarar 2020 kadai, cutar ta yi sanadin mutuwar mata 342,000 daga cikin kimanin 604,000 da aka yi kiyasin sun kamu da ita a shekarar a duk fadin duniya. Kuma kaso 90 cikin dari daga cikinsu, mata ne na kasashe masu matsakaici da karancin kudin shiga.

  • Don Tinkarar Hauhawar Farashi Ake Neman Shiga Tsarin BRICS

Likitocin za su gabatar da kwarewarsu a fannonin bincike da kula da gano cutar ta sankarar bakin mahaifa, tare da horar da takwarorinsu na kasar.

Irin wadannan tallafi da kasar Sin kan bayar ga kasashen Afrika a kai a kai ne dalilin da a koda yaushe na kan kira kasar a matsayin wadda ta san ya kamata kuma sahihiyar aminiya ga kasashen Afrika. Har kullum taimakon kasar Sin ga al’ummar Afrika, taimako ne irin na ’yan uwantaka, na sanin ciwon dan uwa, haka kuma taimako ne na kai tsaye da mutane za su amfana da shi. Zuwan likitocin, tabbas ba karamin taimako zai bayar ba, wajen ceton dimbin rayukan mata da ma karfafawa matan gwiwar zuwa ana duba su tun kafin cutar ta ci karfinsu.

Baya ga haka, yadda tawagar likitocin suka tashi musamman suka zuwa Afrika, zai kara zaburar da mahukuntan nahiyar wajen kara kula da lafiyar mata. Wani abu dake burge ni da kasar Sin shi ne, baya ga mayar da hankali kan kulawa da jama’arta, tana bayar da muhimmanci na musamman ga lafiyar mata. Tuni ta dauki dabarun yaki da wannan cuta mai kisa ta hanyar gudanar da bincike da kulawa, har da samar da rigakafi ’yar kasa.

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Hakika akwai dabaru da darussa da dama da likitocinmu na nahiyar Afrika za su iya koya daga takwarorinsu Sinawa. Fatan ita ce, kwalliya za ta biya kudin sabulu, kana kasar Sin ta fadada wannan taimako zuwa sauran kasashen nahiyar domin ceton karin rayuka. (Fa’iza Mustapha)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
Next Post
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025
Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno

November 4, 2025
Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha

November 4, 2025
China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

China Ta Gargaɗi Amurka Kan Tsoma Baki A Harkokin Nijeriya

November 4, 2025
2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.