ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Likitoci Sinawa A Saliyo Za Ta Ceci Rayukan Dimbin Mata

by CMG Hausa
3 years ago
Likitoci Sinawa

Birnin Freetown na Saliyo ya karbi manyan baki a jiya Litinin, wato tawagar likitocin kasar Sin, da za su taimakawa kasar yaki da cutar sankarar bakin mahaifa. 

Sankarar bakin mahaifa, cuta ce da ta zama abar tsoro a tsakanin mata la’akari da yadda take wahalar da su da kai wa ga asarar rai a karshe. A cewar hukumar lafiya ta duniya, a shekarar 2020 kadai, cutar ta yi sanadin mutuwar mata 342,000 daga cikin kimanin 604,000 da aka yi kiyasin sun kamu da ita a shekarar a duk fadin duniya. Kuma kaso 90 cikin dari daga cikinsu, mata ne na kasashe masu matsakaici da karancin kudin shiga.

  • Don Tinkarar Hauhawar Farashi Ake Neman Shiga Tsarin BRICS

Likitocin za su gabatar da kwarewarsu a fannonin bincike da kula da gano cutar ta sankarar bakin mahaifa, tare da horar da takwarorinsu na kasar.

ADVERTISEMENT

Irin wadannan tallafi da kasar Sin kan bayar ga kasashen Afrika a kai a kai ne dalilin da a koda yaushe na kan kira kasar a matsayin wadda ta san ya kamata kuma sahihiyar aminiya ga kasashen Afrika. Har kullum taimakon kasar Sin ga al’ummar Afrika, taimako ne irin na ’yan uwantaka, na sanin ciwon dan uwa, haka kuma taimako ne na kai tsaye da mutane za su amfana da shi. Zuwan likitocin, tabbas ba karamin taimako zai bayar ba, wajen ceton dimbin rayukan mata da ma karfafawa matan gwiwar zuwa ana duba su tun kafin cutar ta ci karfinsu.

Baya ga haka, yadda tawagar likitocin suka tashi musamman suka zuwa Afrika, zai kara zaburar da mahukuntan nahiyar wajen kara kula da lafiyar mata. Wani abu dake burge ni da kasar Sin shi ne, baya ga mayar da hankali kan kulawa da jama’arta, tana bayar da muhimmanci na musamman ga lafiyar mata. Tuni ta dauki dabarun yaki da wannan cuta mai kisa ta hanyar gudanar da bincike da kulawa, har da samar da rigakafi ’yar kasa.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Hakika akwai dabaru da darussa da dama da likitocinmu na nahiyar Afrika za su iya koya daga takwarorinsu Sinawa. Fatan ita ce, kwalliya za ta biya kudin sabulu, kana kasar Sin ta fadada wannan taimako zuwa sauran kasashen nahiyar domin ceton karin rayuka. (Fa’iza Mustapha)

Likitoci Sinawa
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
Daga Birnin Sin

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
Next Post
NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Tabar Wiwi Buhu 116 A Jihar Kano

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Likitoci Sinawa

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.