ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Don Tinkarar Hauhawar Farashi Ake Neman Shiga Tsarin BRICS

by CMG Hausa
3 years ago
BRICS

A kwanakin nan, hauhawar farashin kayayyaki a tarayyar Najeriya ta yi tsanani, har ma rahotanni na cewa, karuwar farashin kayayyakin abinci ta kai kashi 25%. Ko yaya yanayin farashi a wuraren ku yake? Da fatan babu matsala.

Hakika farashin kayayyaki yana nuna yadda yanayin tattalin arzikin wata kasa yake ciki, kana yana da alaka da yanayin tattalin arziki, da harkokin siyasa na kasa da kasa. Misali, yadda baitulmalin kasar Amurka ke kara ruwan kudin ajiya da na bashi a kai a kai, ya sa darajar kudin kasar wato dalar Amurka, wadda ake yawan yin amfani da ita wajen cinikin kasa da kasa karuwa, lamarin da ya haddasa raguwar darajar kudin sauran kasashe, da tashin gwauron zabin farashin kayayyaki a kasuwanninsu, da karuwar bashin da ake binsu irin na dalar Amurka.

  • Shugaban Aljeriya: Ina Fatan Kasata Za Ta Shiga Tsarin Hadin Gwiwa Na BRICS

Ban da haka, rikicin da ake yi tsakanin kasashen Rasha da Ukraine, da dimbin takunkumin da kasashen yamma ke sakawa sakamakon rikicin, sun haddasa matsalar hauhawar farashin makamashi da hatsi, wadda ita ma ta tsaurara yanayin da kasashe masu tasowa ke ciki na fama da hauhawar farashin kaya.

ADVERTISEMENT

A lokacin da kasashen yamma suka yi biris da moriyar kasashe masu tasowa, ko kuma aka dauki matakan da ka iya lahanta moriyarsu, to tilas ne su kasashe masu tasowa su juya ga tsarin hadin gwiwar da ake yi tsakanin kasashe masu tasowa, don tabbatar da samun isashen goyon baya. Wannan shi ne dalilin da ya sa tsarin BRICS ke janyo hankalin dimbin kasashe masu tasowa. A cewar Anil Sooklal, babban jami’in kasar Afirka ta Kudu mai kula da harkoki masu alaka da tsarin BRICS, wasu kasashe fiye da 40, sun riga sun bayyana niyyarsu ta neman izinin shiga tsarin BRICS, ciki har da dukkan manyan kasashe masu tasowa na duniya.

Wani taro mai alaka da aikin tsaro da ake gudanarwa karkashin laimar tsarin BRICS a kasar Afirka ta Kudu, shi ma ya nuna yadda tsarin ke jan hankalin kasashe daban daban, inda ban da membobin kungiyar 5, wato kasashe Brazil, da Rasha, da Indiya da Sin, da kuma Afirka ta Kudu, sauran kasashen da suka hada da Belarus, da Iran, da Saudiyya, da Masar, da Burundi, da hadaddiyar daular Larabawa ta UAE, da Khazakstan, da Cuba, da dai sauransu, su ma sun tura wakilai don halartar taron.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Kana a cewar kasar Afirka ta Kudu, wadda za ta karbi bakuncin taron koli na BRICS da zai gudana a wata mai zuwa, a taron dake tafe ma za a dora muhimmanci kan tattauna batun habaka tsarin BRICS, inda za a kara yawan mambobinsa.

Hakika kasashe masu tasowa, sun darajanta kokarin da kasashen BRICS suke yi, na maye gurbin dalar Amurka da sauran kudi. Tun daga shekarar 2010, kasashen BRICS sun kaddamar da tsarin hadin gwiwa tsakananin bankunansu, don ba da izinin yin amfani da kudi na kansu wajen gudanar da cinikin kasa da kasa. Kana tsarin BRICS ya bukaci mambobinsa da su kara yin hadin gwiwa ta fuskar kudi da ya shafi musaya, da zuba jari ta kudin kasashen, da dai sauransu, don neman kafa wani tsarin kudi na kasa da kasa da ya kunshi mabambantan kudi na kasashe daban daban. Wannan manufa ta zama tudun-mun-tsira ga dimbin kasashe masu tasowa, wadanda suke fuskantar matsin lamba a fannin tattalin arziki.

Ban da haka, girman kasashen BRICS, da karfin tattalin arzikinsu, su ma sun tabbatar da yiwuwar samun ci gaban tattalin arziki, ta hanyar yin hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Yanzu haka yawan al’ummun kasashen BRICS ya kai kashi 42% cikin jimillar al’ummun daukacin duniya. Kana yawan GDPn kasashen BRICS ya riga ya haura na kungiyar G7, wadda ke kunshe da manyan kasashe masu sukuni guda 7. Haka zalika, bankin neman ci gaba na BRICS, shi ma zai taka rawar samar da kudin musaya bisa bukatar da ake samu cikin gaggawa, don tabbatar da tsaron mambobin kasashe a fannin hada-hadar kudi.

A karshe dai, ana sa ran ganin tsarin BRICS ya zama wani muhimmin dandalin da daukacin kasashe masu tasowa ke iya gudanar da hadin gwiwa a ciki, bisa yadda kasashen Afirka, da sauran kasashe masu tasowa na sauran yankuna ke kokarin neman shiga cikin tsarin.

Ta la’akari da yanayin karuwar kason da kasashen BRICS ke samu cikin tattalin arzikin duniya, hadin gwiwarsu za ta taka muhimmiyar rawa, a fannin kula da harkokin kasa da kasa, da samar da gudummawa ga yunkurin kare zaman lafiya, da raya tattalin arzikin duniya, gami da kafa al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma ta bai daya. (Bello Wang)

BRICS
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Zargin Badaƙala: An Dakatar Da Shugabannin Ƙananan Hukumomi 3 Na Jihar Kaduna

Zargin Badaƙala: An Dakatar Da Shugabannin Ƙananan Hukumomi 3 Na Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.