• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Nancy Pelosi Zuwa Taiwan Takala Ce Mai Muguwar Manufa

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ziyarar Nancy Pelosi Zuwa Taiwan Takala Ce Mai Muguwar Manufa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A daren Talatar 2 ga watan Agustan shekaran nan ne kakakin majalisar wakilan kasar Amurka Nancy Pelosi ta dira a tsibirin Taiwan na kasar Sin, duk da cewa kasar Sin ta gargadi kasar Amurka tun kafin Nancy Pelosi ta tashi daga Amurka.

Wannan halin dai irin na mai kunnen kashi da Amurka ta dauka na shirya ziyarar kakakin majalisa Pelosi dai abu ne wanda ya keta ‘yancin mulkin kasar Sin da tsokana da shiga sharo ba shanu a harkokin cikin gidan kasar.

  • Ziyarar Nancy Pelosi A Yankin Taiwan Ta Tsananta Halin Da Yankin Ke Ciki Tare Da Zubar Da Kimar Amurka A Duniya

Tun farko dai shuwagabanin kasashen biyu na Sin da Amurka wato Xi Jinping da Joe Biden sun tattauna a wayar tarho, inda shugaba Xi ya ja kunnen kasar ta Amurka da cewa duk wanda ya yi wasa da wuta to ya tabbatar da shi za ta kona.

Sanin kowa ne dai cewa kasar Sin daya ce tak a duniya kuma Taiwan yanki ne na kasar, a kan wannan, kasar Amurka ma ba ta musanta haka ba domin Sin da Amurka sun cimma yarjejeniyar kulla huldar diplomasiyya a shekarar 1978, inda Amurkar ta amince da gwamnatin jamhuriyar jama’ar Sin a matsayin halastacciyar gwamnati daya kacal na kasar ta Sin, kuma jama’ar Amurka za ta kiyaye hulda da jama’ar yankin Taiwan ta fannonin al’adu da ta kasuwanci da sauransu, amma ban da ta sassan gwamnati.

Taiwan dai tsibiri ne kuma yanki ne a karkashin jamhuriyar jama’ar Sin wanda yake kudu maso gabashin kasar.

Labarai Masu Nasaba

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Mutanen Taiwan dai Sinawa ne kuma yarensu da al’adunsu duka na Sinawa ne.
Haka kuma kamar yadda muka sani, Taiwan ba kasa mai zaman kanta ba ce kuma ba ta da mazauni a majalisar dinkin duniya MDD ko a kungiyoyin kasa da kasa irin na gwamnati, don haka ma ne, babban sakataren MDD Antonio Guterres ya nuna rashin jin dadinsa da ziyarar Pelosi wadda take neman ta da zaune tsaye da kawo rudani a zaman lafiya a yankin gabashin Asiya da ma duniya baki daya.

Babban sakatare Guterres ya yi bayani cewa za a tsaya tsayin daka kan kudurin kasancewar kasar Sin daya ce tak a duniya.

Kasashe dai fiye da 160 ma suka yi tir da ziyarar Pelosi da nuna goyon bayansu ga kasar Sin da kuma bayyana cewa ziyarar ta keta dokokin kasa da kasa da manufar nan ta kasar Sin daya ce tak a duniya kuma Taiwan yanki ne na kasar Sin.

Wannan ziyara dai a ganina na mai lura da harkokin kasashen waje, babban kuskure ne kasar Amurka ta tafka, kuma takala ce da yin katsalandan a harkokin cikin gida na kasar Sin. Haka zalika, abin lura ne Amurka na yin amfani da gurbatacciyar siyasa a yankin Asiya domin wata manufarta. A sakamakon sa ido da katutu da Amurka ke yi a yankin ya sa kasashe da dama suna yin tir da halayenta na neman fitina.

Hakazalika ban da ta da zaune tsaye da tsokana da wata manufa ban ga amfanin da ziyarar Pelosi za ta kawo wa yankin Taiwan ba da kawo halin zaman doya da man ja a huldar da ke tsakanin kasar Sin da Amurka.

A yanzu haka dai wannan lamari ya jawo ce-ce-ku-ce tsakanin kasar Sin da Amurka a yayin da kasar Sin ta yi martani ta hanyar dakatar da wasu yarjejeniyoyi da ake yi tsakanin kasashen biyu a baya. Ita ma Nancy Pelosi ta samu nata a yayin da kasar Sin ta kakaba mata tare da iyalanta takunkumai da suka dace da tanadin dokokin jamhuriyar jama’ar kasar Sin.

Wannan dai duk abubuwa ne wadanda ya kamata kasar Amurka ta san cewa kasar Sin ba za ta zauna ta yi shiru ba idan aka ci zarafinta ba.

Ya kamata kuma Amurka ta lura cewa Allah wadai da kasashe suka yi a kan wannan ziyara wani abu ne da zai rage mata girmamawa a idon duniya baki daya saboda abin da zai haifar sakamakon ziyarar zai iya shafar kasashen duniya da ba su san hawa ba bare sauka ba. (Lawal Sale)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Saki Tsofaffin Gwamnoni, Dariye Da Nyame Daga Gidan Yarin Kuje

Next Post

“El-Rufai Zai Koma PDP Kafin 2023”

Related

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

16 minutes ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

1 hour ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

3 hours ago
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157
Daga Birnin Sin

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

5 hours ago
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

23 hours ago
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

1 day ago
Next Post
“El-Rufai Zai Koma PDP Kafin 2023”

"El-Rufai Zai Koma PDP Kafin 2023"

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.