• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Shugaba Xi A Turai Ta Kara Bayyana Muradin Sin Na Ganin Tabbatuwar Zaman Lafiya A Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
Xi

Yayin da shugaban Sin Xi Jinping ke ci gaba da ziyara a kasar Faransa, ya tattauna da manema labarai tare da shugaban kasar Emmanuel Macron, a jiya Litinin. Shugaba Xi ya bayyana wasu batutuwan da suka shafi kasa da kasa, kuma daga cikinsu akwai wadanda suka fi jan hankalina su ne:

Na daya, a shirye Sin take ta hada hannu da Faransa wajen amfani da wasannin Olympics a matsayin dandali na wanzar da zaman lafiya a duniya. Ba sai an fada ba, duk mun san yanayi na hargitsi da duniya take ciki yanzu haka, kana mun san irin rawar da wasanni ke takawa wajen ingiza hadin kai da zaman lafiya tsakanin mabanbantan al’ummomi. Hakika kasar Sin ta yi kyakkyawan tunani na amfani da wasannin na duniya, wajen ingiza sulhu tsakanin kasa da kasa. Matasa su ne kashin bayan kowanne al’umma. Don haka, idan ana amfani da dandamali irin na Olympics wajen yayata bukatar zaman lafiya da kyawawan akidu, a nan gaba za a samu al’umma mai fahimta da ganin mutuncin juna, wadanda za su rayu cikin zaman lafiya.

Na biyu, Sin na goyon bayan tattaunawar zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraine. Tabbas kamar yadda shugaban ya fada, maimakon ingiza rikici ko tallafawa rikicin kamar yadda wasu ke yi, kasar Sin ta kasance mai kira da warware rikicin ta hanyar tattaunawa. Tarihi ya nuna cewa sulhu ba ya samuwa sai da tattaunawa, don haka ya dace bangarori masu ruwa da tsaki da ma wadanda ke ci gaba da ruruta wutar rikicin, su mayar da wuka kube, su rungumi mafita mafi dacewa ta hawan teburin sulhu domin samun zaman lafiya mai dorewa.

Na uku, kasar Sin na kira da a dakatar da bude wuta a rikicin Palasdinu da Isra’ila tare da kafa kasashe biyu. Sanin kowa ne Sin ta kasance gaba gaba wajen kiraye-kirayen tsagaita bude wuta ga rikicin. A matsayinta na babbar kasa, har kullum tana goyon bayan samar da zaman lafiya a duniya, tare da kasancewar murya ga masu rauni. Dadewar da aka yi ana takkadama tsakanin bangarorin biyu ya tabbatar da cewa, idan ba samar da kasashe biyu aka yi ba, ba za a taba samun zaman lafiya ba, kuma rikici na iya bazuwa a yankin Gabas ta Tsakiya.

A ganina, hadin gwiwa tsakanin Sin da Faransa, zai taka rawa wajen dakile fito na fito da wasu kasashe ke neman tadawa tsakaninsu da Sin, haka kuma zai dakile bullar kananan rukunonin da ake kafawa da zummar dakilewa ko matsawa wata kasa lamba. Ziyarar shugaban Sin a Turai, ta nuna cewa, Sin ba ta neman kafa rukunin kawaye, sai dai rugumar kowa da kowa domin inganta dunkulewar kasashen duniya, ba tare da wariya ba, domin samar da zaman lafiya mai dorewa. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin
Daga Birnin Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
Next Post
Hauhawar Farashin Siminti: Majalisa Ta Bai Wa Dangote, BUA, Da Sauransu Wa’adin Kwanaki 14 Su Bayyana Gabanta

Hauhawar Farashin Siminti: Majalisa Ta Bai Wa Dangote, BUA, Da Sauransu Wa'adin Kwanaki 14 Su Bayyana Gabanta

LABARAI MASU NASABA

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025
Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

Binciken ‘Yan Sanda Kan Wanda Ake Zargi Da Tawayen “‘Yancin Kan Taiwan” Mataki Ne Na Adalci Don Kare Hadin Kan Kasa

October 29, 2025
Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.