• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Shugaba Xi A Turai Ta Kara Bayyana Muradin Sin Na Ganin Tabbatuwar Zaman Lafiya A Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Ziyarar Shugaba Xi A Turai Ta Kara Bayyana Muradin Sin Na Ganin Tabbatuwar Zaman Lafiya A Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da shugaban Sin Xi Jinping ke ci gaba da ziyara a kasar Faransa, ya tattauna da manema labarai tare da shugaban kasar Emmanuel Macron, a jiya Litinin. Shugaba Xi ya bayyana wasu batutuwan da suka shafi kasa da kasa, kuma daga cikinsu akwai wadanda suka fi jan hankalina su ne:

Na daya, a shirye Sin take ta hada hannu da Faransa wajen amfani da wasannin Olympics a matsayin dandali na wanzar da zaman lafiya a duniya. Ba sai an fada ba, duk mun san yanayi na hargitsi da duniya take ciki yanzu haka, kana mun san irin rawar da wasanni ke takawa wajen ingiza hadin kai da zaman lafiya tsakanin mabanbantan al’ummomi. Hakika kasar Sin ta yi kyakkyawan tunani na amfani da wasannin na duniya, wajen ingiza sulhu tsakanin kasa da kasa. Matasa su ne kashin bayan kowanne al’umma. Don haka, idan ana amfani da dandamali irin na Olympics wajen yayata bukatar zaman lafiya da kyawawan akidu, a nan gaba za a samu al’umma mai fahimta da ganin mutuncin juna, wadanda za su rayu cikin zaman lafiya.

Na biyu, Sin na goyon bayan tattaunawar zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraine. Tabbas kamar yadda shugaban ya fada, maimakon ingiza rikici ko tallafawa rikicin kamar yadda wasu ke yi, kasar Sin ta kasance mai kira da warware rikicin ta hanyar tattaunawa. Tarihi ya nuna cewa sulhu ba ya samuwa sai da tattaunawa, don haka ya dace bangarori masu ruwa da tsaki da ma wadanda ke ci gaba da ruruta wutar rikicin, su mayar da wuka kube, su rungumi mafita mafi dacewa ta hawan teburin sulhu domin samun zaman lafiya mai dorewa.

Na uku, kasar Sin na kira da a dakatar da bude wuta a rikicin Palasdinu da Isra’ila tare da kafa kasashe biyu. Sanin kowa ne Sin ta kasance gaba gaba wajen kiraye-kirayen tsagaita bude wuta ga rikicin. A matsayinta na babbar kasa, har kullum tana goyon bayan samar da zaman lafiya a duniya, tare da kasancewar murya ga masu rauni. Dadewar da aka yi ana takkadama tsakanin bangarorin biyu ya tabbatar da cewa, idan ba samar da kasashe biyu aka yi ba, ba za a taba samun zaman lafiya ba, kuma rikici na iya bazuwa a yankin Gabas ta Tsakiya.

A ganina, hadin gwiwa tsakanin Sin da Faransa, zai taka rawa wajen dakile fito na fito da wasu kasashe ke neman tadawa tsakaninsu da Sin, haka kuma zai dakile bullar kananan rukunonin da ake kafawa da zummar dakilewa ko matsawa wata kasa lamba. Ziyarar shugaban Sin a Turai, ta nuna cewa, Sin ba ta neman kafa rukunin kawaye, sai dai rugumar kowa da kowa domin inganta dunkulewar kasashen duniya, ba tare da wariya ba, domin samar da zaman lafiya mai dorewa. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaFaransaJapan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bincike: Majalisar Kaduna Ta Tattauna Da Tsoffin Kwamishinoni Da Manyan Sakatarori A Gwamnatin el-Rufai 

Next Post

Hauhawar Farashin Siminti: Majalisa Ta Bai Wa Dangote, BUA, Da Sauransu Wa’adin Kwanaki 14 Su Bayyana Gabanta

Related

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

48 minutes ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

2 hours ago
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

13 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

18 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

18 hours ago
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

19 hours ago
Next Post
Hauhawar Farashin Siminti: Majalisa Ta Bai Wa Dangote, BUA, Da Sauransu Wa’adin Kwanaki 14 Su Bayyana Gabanta

Hauhawar Farashin Siminti: Majalisa Ta Bai Wa Dangote, BUA, Da Sauransu Wa'adin Kwanaki 14 Su Bayyana Gabanta

LABARAI MASU NASABA

An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Ministan Tsaro

Ministan Tsaro Ya Yi Gargadin Sake Dawowar Boko Haram Na Barazana Ga Nijeriya

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.