ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ziyarar Shugaba Xi A Turai Ta Kara Bayyana Muradin Sin Na Ganin Tabbatuwar Zaman Lafiya A Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
Xi

Yayin da shugaban Sin Xi Jinping ke ci gaba da ziyara a kasar Faransa, ya tattauna da manema labarai tare da shugaban kasar Emmanuel Macron, a jiya Litinin. Shugaba Xi ya bayyana wasu batutuwan da suka shafi kasa da kasa, kuma daga cikinsu akwai wadanda suka fi jan hankalina su ne:

Na daya, a shirye Sin take ta hada hannu da Faransa wajen amfani da wasannin Olympics a matsayin dandali na wanzar da zaman lafiya a duniya. Ba sai an fada ba, duk mun san yanayi na hargitsi da duniya take ciki yanzu haka, kana mun san irin rawar da wasanni ke takawa wajen ingiza hadin kai da zaman lafiya tsakanin mabanbantan al’ummomi. Hakika kasar Sin ta yi kyakkyawan tunani na amfani da wasannin na duniya, wajen ingiza sulhu tsakanin kasa da kasa. Matasa su ne kashin bayan kowanne al’umma. Don haka, idan ana amfani da dandamali irin na Olympics wajen yayata bukatar zaman lafiya da kyawawan akidu, a nan gaba za a samu al’umma mai fahimta da ganin mutuncin juna, wadanda za su rayu cikin zaman lafiya.

Na biyu, Sin na goyon bayan tattaunawar zaman lafiya tsakanin Rasha da Ukraine. Tabbas kamar yadda shugaban ya fada, maimakon ingiza rikici ko tallafawa rikicin kamar yadda wasu ke yi, kasar Sin ta kasance mai kira da warware rikicin ta hanyar tattaunawa. Tarihi ya nuna cewa sulhu ba ya samuwa sai da tattaunawa, don haka ya dace bangarori masu ruwa da tsaki da ma wadanda ke ci gaba da ruruta wutar rikicin, su mayar da wuka kube, su rungumi mafita mafi dacewa ta hawan teburin sulhu domin samun zaman lafiya mai dorewa.

ADVERTISEMENT

Na uku, kasar Sin na kira da a dakatar da bude wuta a rikicin Palasdinu da Isra’ila tare da kafa kasashe biyu. Sanin kowa ne Sin ta kasance gaba gaba wajen kiraye-kirayen tsagaita bude wuta ga rikicin. A matsayinta na babbar kasa, har kullum tana goyon bayan samar da zaman lafiya a duniya, tare da kasancewar murya ga masu rauni. Dadewar da aka yi ana takkadama tsakanin bangarorin biyu ya tabbatar da cewa, idan ba samar da kasashe biyu aka yi ba, ba za a taba samun zaman lafiya ba, kuma rikici na iya bazuwa a yankin Gabas ta Tsakiya.

A ganina, hadin gwiwa tsakanin Sin da Faransa, zai taka rawa wajen dakile fito na fito da wasu kasashe ke neman tadawa tsakaninsu da Sin, haka kuma zai dakile bullar kananan rukunonin da ake kafawa da zummar dakilewa ko matsawa wata kasa lamba. Ziyarar shugaban Sin a Turai, ta nuna cewa, Sin ba ta neman kafa rukunin kawaye, sai dai rugumar kowa da kowa domin inganta dunkulewar kasashen duniya, ba tare da wariya ba, domin samar da zaman lafiya mai dorewa. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Xi
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

MASU ALAKA

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Next Post
Hauhawar Farashin Siminti: Majalisa Ta Bai Wa Dangote, BUA, Da Sauransu Wa’adin Kwanaki 14 Su Bayyana Gabanta

Hauhawar Farashin Siminti: Majalisa Ta Bai Wa Dangote, BUA, Da Sauransu Wa'adin Kwanaki 14 Su Bayyana Gabanta

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

Hadin Gwiwar Hada-Hadar Ba Da Hidima Tsakanin Sin Da Afirka Na Karfafa Karfin Afirka

September 11, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

Dalilan Da Ya Sa Jam’iyyun Siyasa Suka Jinkirta Ƙaddamar Da Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen

September 11, 2026
Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

Nazarin CGTN: Kungiyar BRICS Tana Kara Taka Rawar Gani A Harkokin Duniya

September 11, 2026
Za A Ci ’Yan Siyasa Masu Kalaman Ɓatanci Tarar Miliyan 10 Da Ɗaurin Watanni 12 — INEC

2027: A Karon Farko INEC Za Ta Ƙaddamar Da Na’urar Bibiyar Zaɓen Nijeriya

September 11, 2026
Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

Me Ya Sa Kamfanonin Amurka Ke Kyautata Zato Ga Sabuwar Damar Sin?

September 11, 2026
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026  Mrs Zubaida Umar

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Gwamnati Ta Shekarar 2026 Mrs Zubaida Umar

September 11, 2026
Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026
Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Sanata yari

Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari

September 11, 2026
Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.