Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning, ta gabatar da cewa, shugaba Xi Jinping zai halarci taron kolin kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai, zai kuma kai ziyara a kasashen Kazakhstan da Uzbekistan.
Ta bayyana cewa, wannan ziyara shi ne muhimmin aikin diflomasiyya da shugaban kasar Sin ya gudanar a gabanin babban taron wakilan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 20, wanda ke nuna cikakken muhimmancin da bangaren Sin yake dorawa kan kungiyar SCO da alakar kasar Sin da Uzbekistan da kuma Kazakhstan. (Mai fassarawa: Ibrahim daga CMG Hausa)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp