• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zuba Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku Da Japan Ke Shirin Yi Zai Illata Duk Fadin Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
Nukiliya

Gobe ranar teku ce ta kasa da kasa karo na 15, babban taron MDD karo na 63 ya tsai da ranar 8 ga watan Yunin kowace shekara ranar teku ta kasa da kasa, don jan hankalin duniya muhimmancin kiyaye teku, wanda ke da babbar ma’ana ga bunkasuwar al’umma.

Amma a abin takaici ne, albarkacin wannan muhimmiyar rana, kasar Japan har yanzu tana kare aniyarta ta zuba ruwan dagwalon nukiliya ta tashar nukiliya ta Fukushima cikin teku bisa son kanta. Kwanan nan, kafar NHK ta kasar Japan ta ba da labarin cewa, an riga an fara zuba ruwan teku cikin bututun da ruwan dagwalon nukiliya zai bi a Fukushima.

  • An Bude Taron Kasa Da Kasa Na Baje Kolin Harkokin Al’adu A Shenzhen

Shirin nan na Japan ya jawo suka daga gida da ma waje, sai dai gwamnatin Japan ta yi ta neman wanke kanta ta kowa ce hanya.

Gwamnatin Japan ta ce ruwan dagwalon ba zai kawo illa ga muhallin teku ba, amma ko hakan gaskiya ne? A hakika, ruwan dagwalon tashar Fukushima na kunshe da sinadaran nukiliya masu guba sama da 60. Kamfanin samar da wutar lantarki na Tokyo ya ba da wani rahoto a ran 5 ga wata cewa, an gano abin tiriri na Cesium a jikin nau’in kifin da aka kama a gulf din tashar nukiliya ta Fukushima, yawansa ya ninka sau 180 bisa na ma’aunin da aka tanada.

A sa’i daya kuma, igiyar ruwa a wannan wuri na da karfi matuka, matakin da ya sa idan an zuba ruwan dagwalon nukiliya cikin teku, zai yadu zuwa duk fadin tekun duniya a cikin shekaru 10 masu zuwa, abin da zai kawo babbar illa ga muhallin teku da lafiyar jikin Bil Adama.

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Bisa dokar kasa da kasa, ruwan dagwalon nukiliya na Fukushima shara ce, dole ne a ajiye su a maimakon zuba su a cikin teku. Misali a tashar samar da wutar lantarki ta amfani da karfin nukiliya ta kasar Faransa, an kafa cibiyar adana sharar da tashar ke samarwa, matakin da ya fi dacewa.

Gwamnatin Japan ta fitar da shirye-shirye da dama game da yadda za a yi da ruwan dagwalon nukiliya na tashar Fukushima tun daga shekarar 2013, amma daga karshe ta zabi wannan shiri maras imani don yin tsimin kudi da kare kanta.

Shin ko gwamnatin Japan ba ta da isashen kudi? A’a, ba ta da imani ne! Matakin ta zai kawowa muhalli matukar barazana, har ma ya illata makomar Bil Adama baki daya. (Mai zana da rubuta: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
Daga Birnin Sin

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Next Post
Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai – Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

Hajjin Bana: Ku Zama Jakadu Na Kwarai - Gwamnan Gombe Ga Maniyyata

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

October 13, 2025
Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

October 13, 2025
Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.