• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Al’umma: Ƙungiyar GMBNI Ta Karrama Ma’aikacin LEADERSHIP Da Wasu

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Ci Gaban Al’umma: Ƙungiyar GMBNI Ta Karrama Ma’aikacin LEADERSHIP Da Wasu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyar Fafutukar Tabbatar da Ci Gaban Nijeriya ta ‘Grassroots Mobilizers For Better Nigeria Initiatiɓe (GMBNI)’ ta karrama ma’aikacin Rukunin Kamfanonin LEADERSHIP, Rabiu Ali Yusuf da wasu mutane haziƙai da lambar yabo bisa gudunmawarsu ga ci gaban al’umma.

Kwamitin gudanarwa na ƙungiyar na ƙasa ƙarƙashin ingantaccen jagorancin Ambasada Dakta Fatima Mohammed Goni fgau, shugabar ƙungiyar ta ƙasa ne ya yi zama na musamma domin zaƙulo haziƙan mutane inda ta amince da girmama su da lambar yabo don nuna goyon baya, sadaukarwa, da kuma gagarumar gudunmawar da suke bayarwa ga ƙungiyar.

Daga cikin waɗanda suka lambar yabon akwai ‘yan jarida waɗanda an karrama su ne bisa cancanta da jajircewarsu a ayyukansu.

  • Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Da take jawabi a yayin bayar da lambobin yabon Ambasada Fatima Muhammad Goni ta ce, waɗannan jama’a da muka a ƙarƙashin ƙungiyar da nake shugabanta (GMBNI), mun karrama su ne saboda jajircewarsu a wannan ƙungiya wajen ganin ta cimma burin da ta sa a gaba.

Mun yi abubuwa da dama wanda kuma duniya ta gani, kuma muna gode wa Allah da ya kawo mu wannan lokaci, ina yi wa kowa fatan alheri da addu’ ar Allah ya zaunar da ƙasarmu lafiya. Ga dai jerin sunayen mutanen da wannan ƙungiya ta karrama da lambar girma kamar haka.
1Jodah Makinta, Darakta kuma Kodinetan tsare-tsare na Jihar Nasarawa. Sai kuma Kwamared Salihu Abdulhamid Dembos, Darakta Janar na Gidan Talabijin na ƙasa NTA. Akwai Lawan Modu Bama, Mataimaki na musamman ga Suhgaba kuma wacce ta kafa ƙungiyar kan ayyuka na musamman, akwai Nancy Habila Mai Ba Da Shawara ta Musamman ga Shugabn ƙungiyar ta ƙasa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Sharhabil Iliya, Mataimaki na Musamman ga shugabar ƙungiyar ta ƙasa akan harkokin yaɗa labarai. John Ola Zach, Shugaban masu ɗaukar hoto ga shugaban ƙunyar ta ƙasa.

Injiniya.Abdullahi Aliyu. Ambasada Ahmed Umar Bolori, Mataimakin Shugaban Makranta. Lt Col. SJ Dibal, Daraktan Tsaro da Bayar da Bayanan Sirri.

Sauran su ne, Barista Umar Alhaji Bukar, Daraktan Harkokin Shari’ a. Hajiya Hassana Shuaibu Abbas, Kodineta ta Abuja, Abbas Rufai, kodineta na Jihar Jigawa. Gidan Talabijin na Liberty. Timothy T. Kosuga Mai Ba Da Shawara na musamman ga shugaban ƙungiya ta ƙasa a fannin fasaha.

Har ila yau shi ma Musa Aminu, ya samu lambar yabon haziƙin ɗan jarida da Injiniya Kamilu Nasiru Abubakar, Mai Ba Da Shawara na ƙasa.

Modu Bukar, Mai Ba Da Shawara na Musamman ga shugabar ƙungiyar kan al’amuran ilimi. Muhammad Hassan Umar, Mataimaki na Musamman ga Shugabar ƙungiyar akan Kula da harkokin baƙi.

Har ila yau akwai Abdulkarim Kayama Abdullahi, Kodineta na Jihar Yobe, Hajiya Medina Dauda Nadabo, Kodineta kuma jami’a a Shirin da Aliyu Tanko, Shugaban Sashen Hausa na BBC, da Uwaisu Abubakar Idris, Wakilin Gidan Rediyo da Talabijin na Deutche Welle Abuja, sai Apostle B.O Anana, Mai Ba Da Shawara na ƙasa.

Sauran su ne Alhaji Aliyu Musa Turaki, Mai Ba Da Shawara Na ƙasa. Fatima Damagudu Ibellogo, Kodineta na Jihar Binuwai. Hon. Aminu Mohammed Makko, Kodineta na Jihar Gombe. Bwalmo Dubi Abraham, Kodinetan Jihar Adamawa. Suleiman Ibrahim Ali, Kodinetan Jihar Kaduna. Kwamared Mahmood Yayale Nasir, Tsohon Kodinetan Jihar Bauchi.

Haka nan an karrama Dakta Aminu Safana Aliyu, Kodinetan Jihar Katsina. Dakta Abasiama Isidore, Kodinetan Jihar Akwa Ibom. Yusuf Sani Abdullahi, Kodinetan Jihar Filato. Hajiya Maryam Eli Pawa. Kasim Jodah Awi, Mai Ba Da Shawara ga Shugabar ƙungiyar Kan Harkokin Matasa. Muktar Danmaje, Kodinetan a yankin Kudu maso Yamma. Rabiu Ibrahim Abdullahi, Mataimakin Daraktan Tsare-tsare. Zubairu Babangida, Mataimakin Shugaban Masu ɗaukar Hoto ga Shugabar ƙungiyar ta ƙasa

Mahmud Abubakar, Mai Ba Da Shawara na Musamman ga Shugabar ƙugiyar na ƙasa Akan Al’ amuran Gida. Abdullahu Ayuba Ansari, Mai Sanya Ido. Bala Mbaya, Jami’in sa kai. Aisha Umar Jami’ar Sa kai. Lawal Mohammed Abdul (Late Lawal Family), Kodinetan Osun. Mardiyya Adamu (Iyalin Marigayi Auwal, Shugaban Direbobin Shugabar ƙungiya na ƙasa.

Kazalika, ƙungiyar ta karrama manya-manyan malaman tsangaya da suka ba da gudunmawa wajen addu’ o’ i ba dare ba rana, a ƙarƙashin jagorancin Ambsada Fatima Muhammad Goni Shugabar ƙungiyar ta ƙasa kuma wacce ta kafa ƙungiyar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Al'ummaKarramawaƘungiyaYabo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abba Gida-Gida Ya Jagoranci Rusa Wani Gini Mai Hawa 3 Dauke Da Shaguna 90 A Kano

Next Post

Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

48 minutes ago
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
Labarai

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

4 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

6 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

8 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

9 hours ago
Next Post
Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara

Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban

September 17, 2025
Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

September 17, 2025
An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 

September 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

September 17, 2025
Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

Har Kullum Burin Sin Shi Ne Wanzar Da Daidaito Da Cimma Moriya Tare Da Amurka

September 17, 2025
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.