ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bello Matawalle Ya Wawashe Kudi Da Motocin Gwamnati — Gwamnatin Zamfara

by Muhammad
3 years ago
Bello Matawalle

Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana sanarwar da jam’iyyar APC reshen jihar ta fitar a matsayin magagin faduwar jam’iyyar zabe da har yanzu ba ta farfado daga zafin shan kaye ba.

Bayanin na APC dai martani ne ga furucin da Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya yi, inda ya yi kan tsohon Gwamna, Bello Mohammed Matawalle, kan zargin satar motoci da wasu kayayyaki masu daraja a gidan gwamnatin jihar da ke Gusau.

  • Maganar Gwamnan Zamfara Dauda Ya Mallaki Tiriliyan 9 Ba Gaskiya Ba Ne Bata Da Tushe
  • Gwamnan Zamfara Ya Yi Naɗe-naɗen Waɗanda Za Su Taimaka Masa

Gwamnatin jihar Zamfara a cikin wata sanarwa da ta fitar a Gusau a ranar Asabar, ta hannun mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ta yi nuni da cewa yunƙurin da jam’iyyar APC reshen Zamfara ta yi a na ƙoƙarin ba watsohon Gwamna Matawalle kariya ta kowane hali ya kara tabbatar da cewa jam’iyyar ta shiga cikin rudani da hauragiya.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kara da cewa: “Gwamnatinmu ta kuduri aniyar cika alkawuran yakin neman zabe da ta yi wa al’ummar jihar Zamfara, wanda ya hada da gaggauta kwato kudaden jama’a da dukiyoyin da aka sace.

“Maganar jam’iyyar APC na nufin kawar da kai ne kawai daga yin aikin da ya shafi inganta rayuwar jama’a. Lokacinmu yana da daraja, kuma ba za mu iya ɓata shi ba wajen cece-kuce da jam’iyyar da ta shafe shekaru huɗu ba tare da wani aiki ɗaya mai amfani ga al’ummar Zamfara ba, a maimakon haka kawai abin da suka yi shi ne wawushe dumbin dukiyar jihar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

“Muna da hujjoji da bayanan da suka fallasa rashin dacewar Matawalle. Ina karyar take? Tsohon gwamnan ya bayar da kwangilar sayen motocin da za a raba wa manyan ma’aikatu da hukumomi kan kudi biliyan daya da miliyan dari da arba’in da tara da miliyan dari takwas (N1) ,149,800,000.00).

An bayar da kwangilar siyan motocin ga Hafkhad Properties and Facilities Management Nig. LTD. Da nufin amfani da kudin wajen sayan Toyota Lexus VIP Bullet Proof 2021 Model da Toyota Land Cruiser VIP Bullet Proof 2021 Model da kuma Model Toyota Prado V6 2021 da Model Toyota Prado V4 2021 Samfurin Peugeot 2021 da Model Toyota Hilux 2021 sai kuma Toyota Land Cruiser Bullet Hujja 2021 da Toyota Lexus 2021 Model.

“A ranar 4 ga Oktoba, 2021 tsohon gwamnan ya biya MUSACO kudin sayo mota kirar Jeep guda uku kan kudi N484, 512, 500.00; don samar da nau’ikan Prado Jeep guda bakwai masu hana harsashi, da Land Cruiser akan kudi N459, 995, 000.00; don samar da Toyota Hilux guda bakwai akan kudi N228, 830, 000.00.

“A ranar 19 ga Mayu, 2021, Matawalle ya biya kudin samar da Peugeot 406 set 30 ga TK Global Services akan kudi N61,200,000.00. Hakanan a ranar 15 ga Disamba, 2021, an biya Nadeen Butta don samar da Land Cruiser mai hana shigar harsashi a kan N130, 000, 000.00.

“A ranar 26 ga watan Fabrairun 2022, an biya wani dan kwangila Dapiyau B. Linus kudi N160,000,000.00 domin samar da mota kirar Land Cruiser Jeeps 2021; A ranar 20 ga Maris, 2022, gwamnatin Matawalle ta biya MUSACO kudi N120,000,000.00 don samar da motoci guda uku na ofishin Mataimakin Gwamna.”

“Abin takaici ne ga jam’iyyar APC ta Zamfara ta ci gaba da cewa uffan a daidai lokacin da Gwamna mai barin gado da mukarrabansa suka wawashe duk motocin da ke gidan gwamnatin. Wannan abin kunya ne, ba wai jam’iyyar APC ta jiha kadai ba, ga duk wanda Matawalle ya dauka.

“Mun sanar da tsohon Gwamna Bello Matawalle da mataimakinsa a hukumance cewa su dawo da dukkan motocin da suka sata cikin kwanakin aiki biyar. Cewar Sulaiman a madadin gwamnatin Zamfara.

Bello Matawalle
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Bello Matawalle
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Ƴan Sanda A Gombe Sun Kama Matasa 11 Da Ake Zargi Da Kalare

Ƴan Sanda A Gombe Sun Kama Matasa 11 Da Ake Zargi Da Kalare

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.