• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Sanda A Gombe Sun Kama Matasa 11 Da Ake Zargi Da Kalare

by Leadership Hausa
2 years ago
Gombe

Rundunar Ƴan Sanda a Jihar Gombe ta kama wasu matasa 11 da ake zargi da Kalare tare da mallakar muggan makamai.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ASP Mahid Mu’azu Abubakar ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya miƙa wa LEADERSHIP Hausa.

  • ‘Ƴansanda Sun Kama Mutane 12 Bisa Zarginsu Da Laifuka Daban-Daban A Gombe
  • APC Ta Dakatar Da Sanata Bulus A Gombe Kan Zargin Yi Mata Zagon Kasa

Ya bayyana sunayen waɗanda ake zargin da cewa sun haɗa da: Abdullahi Saleh mai shekaru 18, da Yusuf Shitu mai shekaru 18, da Musa Saleh mai shekaru 20, sai Usman Suleiman mai shekaru 23.

Mahid Muazu yace sauran sune: Alhassan mai shekaru 19, da Aliyu Yakubu ɗan shekara 21, da Sadiq Adamu mai shekaru 21, sai Dauda Ibrahim da Haruna Mohammed mai shekara 18.

Jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan ya ce, “A ranar 30 ga watan Mayun 2023, da misalin karfe 5:30 na yamma, al’ummomin anguwannin Pantami, da Malam-Inna, da Tudun-Wada da kuma Checheniya dake cikin garin Gombe, sun kai rahoto a ofishin Operation Hattara cewa wassu gungun matasa da ake zargin ƴan Kalare ne sun addabi anguwannin nasu da aika-aikar munanan laifuka”.

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Yace samun wannan ƙorafi ke da wuya rundunar ta Operation Hattara ta kai farmaki maɓoyar ƴan Kalaren a wurare daban-daban, inda suka yi nasarar cafke waɗanda ake zargin.

ASP Mahid Abubakar ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

Ya ƙara da cewa, “Makaman da muka kwato sun haɗa da adduna guda bakwai da wuƙaƙe guda uku”.

ASP Mahid Mu’azu ya yi ƙira ga al’ummar jihar su riƙa haɗa kai da ƴan sanda a ko da yaushe don inganta tsaron lafiyarsu ta hanyar bada bayanai masu amfani ga jami’an tsaro game da duk wani motsin da basu gamsu da shi ba.

Ya ƙara da cewa al’ummar jihar suna iya ƙiran lambobin gaggawa don kai rahoton duk wata matsalar tsaro a jihar. Yace lambobin su ne: 08150567771 ko 09165472923.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100
Labarai

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
Next Post
Kungiyoyin Da Suka Fi Samun Katin Gargadi A Gasar Firimiya Ta Bana

Kungiyoyin Da Suka Fi Samun Katin Gargadi A Gasar Firimiya Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Gombe

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.