ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƴan Sanda A Gombe Sun Kama Matasa 11 Da Ake Zargi Da Kalare

by Leadership Hausa
3 years ago
Gombe

Rundunar Ƴan Sanda a Jihar Gombe ta kama wasu matasa 11 da ake zargi da Kalare tare da mallakar muggan makamai.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ASP Mahid Mu’azu Abubakar ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya miƙa wa LEADERSHIP Hausa.

  • ‘Ƴansanda Sun Kama Mutane 12 Bisa Zarginsu Da Laifuka Daban-Daban A Gombe
  • APC Ta Dakatar Da Sanata Bulus A Gombe Kan Zargin Yi Mata Zagon Kasa

Ya bayyana sunayen waɗanda ake zargin da cewa sun haɗa da: Abdullahi Saleh mai shekaru 18, da Yusuf Shitu mai shekaru 18, da Musa Saleh mai shekaru 20, sai Usman Suleiman mai shekaru 23.

ADVERTISEMENT

Mahid Muazu yace sauran sune: Alhassan mai shekaru 19, da Aliyu Yakubu ɗan shekara 21, da Sadiq Adamu mai shekaru 21, sai Dauda Ibrahim da Haruna Mohammed mai shekara 18.

Jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan ya ce, “A ranar 30 ga watan Mayun 2023, da misalin karfe 5:30 na yamma, al’ummomin anguwannin Pantami, da Malam-Inna, da Tudun-Wada da kuma Checheniya dake cikin garin Gombe, sun kai rahoto a ofishin Operation Hattara cewa wassu gungun matasa da ake zargin ƴan Kalare ne sun addabi anguwannin nasu da aika-aikar munanan laifuka”.

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Yace samun wannan ƙorafi ke da wuya rundunar ta Operation Hattara ta kai farmaki maɓoyar ƴan Kalaren a wurare daban-daban, inda suka yi nasarar cafke waɗanda ake zargin.

ASP Mahid Abubakar ya ce nan ba da jimawa ba za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

Ya ƙara da cewa, “Makaman da muka kwato sun haɗa da adduna guda bakwai da wuƙaƙe guda uku”.

ASP Mahid Mu’azu ya yi ƙira ga al’ummar jihar su riƙa haɗa kai da ƴan sanda a ko da yaushe don inganta tsaron lafiyarsu ta hanyar bada bayanai masu amfani ga jami’an tsaro game da duk wani motsin da basu gamsu da shi ba.

Ya ƙara da cewa al’ummar jihar suna iya ƙiran lambobin gaggawa don kai rahoton duk wata matsalar tsaro a jihar. Yace lambobin su ne: 08150567771 ko 09165472923.

Gombe
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala
Labarai

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON
Labarai

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Next Post
Kungiyoyin Da Suka Fi Samun Katin Gargadi A Gasar Firimiya Ta Bana

Kungiyoyin Da Suka Fi Samun Katin Gargadi A Gasar Firimiya Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.