• English
  • Business News
Tuesday, July 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙone-ƙonen Da Ƴan Ta’adda Ke Yi Zai Ƙara Haifar Da Ƙarancin Abinci

by Idris Aliyu Daudawa and Jibrin Baba Ndace
8 months ago
in Labarai
0
Ƙone-ƙonen Da Ƴan Ta’adda Ke Yi Zai Ƙara Haifar Da Ƙarancin Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Al’amarin yadda ‘yan ta’adda suke cin karensu babu ko babbaka abin yana da matukar daure kai domin kuwa suna yin abubuwan da suka ga dama, su kashe manoma, su kona gonakinsu, ko su kwashe  masu kayan amfanin gonarsu, kai sai dai abinda suka ga damar yi. Yanzu dai ba karamar illa ko matsala suke bada gudunmawa ba ta wajen karancin abinci.

Gaba dayan Jihohin Arewa kadan ba su fusknatar irin wannan halin in ma da akwi su, sai dai kawai ace irin cin fuskar da suke yi a wadancan wuraren sun sha bamban dana wadansu wurare sai daia yi fatan Allah ya taiamaka mana wajen kawo karshen ta’asar da suke yi, da a karshe take samar da karancin abinci.

  • Yanayin Cin Abinci Da Baccin Annabi Muhammadu (SAW)
  • Gwamnatin Bauchi Ta Kaddamar Da Kwamitin Adana Kayan Abinci

Ta irin hakan ne yanzu an samu dalilai da suka sa aka kona gonakin masara na wasu al’umma a karamar hukumar Birnin Gwari ta Jihar Kaduna, barnar da ‘yan ta’adda ne suka yi ta.

Shugaban  kungiyar ci gaban masarautar Birnin-Gwari  (BEPU), Ishak Usman Kasai, wanda kuma har ila yau shine shugaban kungiyar al’ummomin da suke bakin iyaka, a hirar da yayi da manema labarai ya bayyana cewa da akwai wani  abinda ya faru wanda ya shafi yarjejeniyar da aka yi ta zaman lafiya.

Kamar yadda yace, “Wurin da jamia’an tsaro suka kawo zaman lafiya a kokarin da suke yi shine babbar hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari.Amma idan ana maganar kauyuka ne babu wani abinda aka yi a wuraren da za ‘a iya cewa sun taimaka hare- haren sun ja da baya.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

“Dan haka abinda ya far ranar Lahadi ta makon daya gabata inda wasu ‘yan ta’adda suka kona wasu gonaki kan hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari, shine wasu wurare kusa da Kwoga, Zoko da kuma Gayam. Wurin da akwai wani azabibin shugaban’ dan ta’adda wanda ake kira da suna Yellow Janbros.

“Akwai wani jami’in soja a wurin wanda yana  yin duk abubuwan da suka kamata domin ya samu hanyar gamawa da ‘yan ta’addar wadanda suke bi ta hanyar shanu  zuwa Zamfara, ta Birnin Gwari zuwa Jihar Neja domin kawai su je su kai hare- hare.

Jami’in soja shi da tawagar ta sa sun samu gamawa da wasu ‘yan kungiyar Yellow Janbros. Mako biyu da suka wuce, jami’in sojan ya jagoranci tawagarsa inada suka kai samame lokacin da ‘yan ta’addar suke wucewa daga Neja domin su shiga Birnin Gwari.

“Sanadiyar abinda sojojin suka yi masu ne yasa suka saw a gonakin masarar wuta ranar Lahadi kusa da wurin. Sun yi hakan ne inda suka fadawa mutanen da suke wurin, su zo su sake yin wata yarjejeniyar zaman lafiya, ko kuma su ci gaba da kai masu hare- hare.Da suka ji hakan ne fa sai su al’ummar wurin suka fara tunanin hanyoyin da za su taimakawa jami’an soja su gama da ‘yan ta’adda.

“Maganar gaskiya abinda ya kawo tsaikon rashiun zaman lafiya ya fara ne tun arangamar da suka yi da soja suka yi masu luguden wuta, da lalacewar yarjejeniyar zaman lafiya ta sa su ‘yan ta’addar suka zafafa kai hare- hare a gonakin manoma”.

Kafin dai akai harin na ranar Lahadi, “akwai wani Malamin addini daga sashen Bauchi da Gombe, da ake kiransa Azadu Sunnah, wanda ya zo Birnin Gwari ranar Asabar saboda a samu ayi lamarin daya shafi  yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin ‘yan ta’adda da mutanen garin, amma kuma ranar Lahadi sai su ka kai wa mutanen wuriin hari.

“Idan ko muddin dai ana bukatar garin Birnin Gwari da gaba dayan sashen Arewa maso yamma su samu zaman lafiya, kamata yayi gwamnati ta tura sojoji zuwa dajin Kuduru, tsakanin Chikun da Birnin Gwari, a tura soja zuwa dajin Kamuku da dajin Kuyanbana  tsakanin  Dan Sadau a Jihar Zamfara da Kaduna , aje dajin Kuzamani akan iyaka Kaduna da Neja”.

Sai dai kuma a dukkan wuraren nkamar yadda ya jaddada, “A dukkan wuraren akwai kungiya- kungiya ta ‘yan ta’adda wadanda suka kai muatane zuwa dazuzzukan,  ga shi kuma babu isassun jami’an tsaro a wuraren da suke da hatsari. Don haka akwai bukatar a shirya rundunar tsaro ta hadin gwiwa tskanin Jiha da Jiha a Jihohin, Kaduna, Neja da Zamfara.Abinda ya kamata ayi ke nan ba kawai a tsaya kan hanya ba ko kuma wasu wuraren al’umma .


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rayuwar Annabi Muhammadu (SAW) Da Abin Da Ya Ta’allaka Da Aurensa (2)

Next Post

GORON JUMA’A 22/11/2024

Related

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom
Labarai

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

1 hour ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Manyan Labarai

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

2 hours ago
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
Da ɗumi-ɗuminsa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

11 hours ago
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci
Da ɗumi-ɗuminsa

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

12 hours ago
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

15 hours ago
Kakakin Majalisar Wakilai, Abbas, Ya Yi Jimamin Rasuwar Buhari, Ya Ce Mutuwa Ce Da Ta Girgiza Shi
Da ɗumi-ɗuminsa

SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

17 hours ago
Next Post
GORON JUMA’A 22/11/2024

GORON JUMA'A 22/11/2024

LABARAI MASU NASABA

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom

July 29, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati

July 29, 2025
An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

An Gudanar Da Taron Dandalin Tattaunawar Neman Sabon Tunani Na Asali Na 2025

July 28, 2025
Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa

July 28, 2025
Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

Sin: Ya Kamata A Warware Sabanin Tattalin Arziki Da Cinikayya Ta Hanyar Tattaunawa

July 28, 2025
Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

Kotun Ta Ci Tarar Hukumar NYSC Kan Haramtawa ‘Yan Bautar Ƙasa Mata Sanya Siket Da Tauye Musu ‘Yanci

July 28, 2025
An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

An Fara Sabon Zagayen Tattaunawar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka A Sweden

July 28, 2025
Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Iska Mai Ni’ima Da Ruwa Mai Inganci A Rabin Farko Na Bana

July 28, 2025
Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar

July 28, 2025
Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje

July 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.