ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙone-ƙonen Da Ƴan Ta’adda Ke Yi Zai Ƙara Haifar Da Ƙarancin Abinci

by Idris Aliyu Daudawa and Jibrin Baba Ndace
2 years ago
Abinci

Al’amarin yadda ‘yan ta’adda suke cin karensu babu ko babbaka abin yana da matukar daure kai domin kuwa suna yin abubuwan da suka ga dama, su kashe manoma, su kona gonakinsu, ko su kwashe  masu kayan amfanin gonarsu, kai sai dai abinda suka ga damar yi. Yanzu dai ba karamar illa ko matsala suke bada gudunmawa ba ta wajen karancin abinci.

Gaba dayan Jihohin Arewa kadan ba su fusknatar irin wannan halin in ma da akwi su, sai dai kawai ace irin cin fuskar da suke yi a wadancan wuraren sun sha bamban dana wadansu wurare sai daia yi fatan Allah ya taiamaka mana wajen kawo karshen ta’asar da suke yi, da a karshe take samar da karancin abinci.

  • Yanayin Cin Abinci Da Baccin Annabi Muhammadu (SAW)
  • Gwamnatin Bauchi Ta Kaddamar Da Kwamitin Adana Kayan Abinci

Ta irin hakan ne yanzu an samu dalilai da suka sa aka kona gonakin masara na wasu al’umma a karamar hukumar Birnin Gwari ta Jihar Kaduna, barnar da ‘yan ta’adda ne suka yi ta.

ADVERTISEMENT

Shugaban  kungiyar ci gaban masarautar Birnin-Gwari  (BEPU), Ishak Usman Kasai, wanda kuma har ila yau shine shugaban kungiyar al’ummomin da suke bakin iyaka, a hirar da yayi da manema labarai ya bayyana cewa da akwai wani  abinda ya faru wanda ya shafi yarjejeniyar da aka yi ta zaman lafiya.

Kamar yadda yace, “Wurin da jamia’an tsaro suka kawo zaman lafiya a kokarin da suke yi shine babbar hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari.Amma idan ana maganar kauyuka ne babu wani abinda aka yi a wuraren da za ‘a iya cewa sun taimaka hare- haren sun ja da baya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

“Dan haka abinda ya far ranar Lahadi ta makon daya gabata inda wasu ‘yan ta’adda suka kona wasu gonaki kan hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari, shine wasu wurare kusa da Kwoga, Zoko da kuma Gayam. Wurin da akwai wani azabibin shugaban’ dan ta’adda wanda ake kira da suna Yellow Janbros.

“Akwai wani jami’in soja a wurin wanda yana  yin duk abubuwan da suka kamata domin ya samu hanyar gamawa da ‘yan ta’addar wadanda suke bi ta hanyar shanu  zuwa Zamfara, ta Birnin Gwari zuwa Jihar Neja domin kawai su je su kai hare- hare.

Jami’in soja shi da tawagar ta sa sun samu gamawa da wasu ‘yan kungiyar Yellow Janbros. Mako biyu da suka wuce, jami’in sojan ya jagoranci tawagarsa inada suka kai samame lokacin da ‘yan ta’addar suke wucewa daga Neja domin su shiga Birnin Gwari.

“Sanadiyar abinda sojojin suka yi masu ne yasa suka saw a gonakin masarar wuta ranar Lahadi kusa da wurin. Sun yi hakan ne inda suka fadawa mutanen da suke wurin, su zo su sake yin wata yarjejeniyar zaman lafiya, ko kuma su ci gaba da kai masu hare- hare.Da suka ji hakan ne fa sai su al’ummar wurin suka fara tunanin hanyoyin da za su taimakawa jami’an soja su gama da ‘yan ta’adda.

“Maganar gaskiya abinda ya kawo tsaikon rashiun zaman lafiya ya fara ne tun arangamar da suka yi da soja suka yi masu luguden wuta, da lalacewar yarjejeniyar zaman lafiya ta sa su ‘yan ta’addar suka zafafa kai hare- hare a gonakin manoma”.

Kafin dai akai harin na ranar Lahadi, “akwai wani Malamin addini daga sashen Bauchi da Gombe, da ake kiransa Azadu Sunnah, wanda ya zo Birnin Gwari ranar Asabar saboda a samu ayi lamarin daya shafi  yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin ‘yan ta’adda da mutanen garin, amma kuma ranar Lahadi sai su ka kai wa mutanen wuriin hari.

“Idan ko muddin dai ana bukatar garin Birnin Gwari da gaba dayan sashen Arewa maso yamma su samu zaman lafiya, kamata yayi gwamnati ta tura sojoji zuwa dajin Kuduru, tsakanin Chikun da Birnin Gwari, a tura soja zuwa dajin Kamuku da dajin Kuyanbana  tsakanin  Dan Sadau a Jihar Zamfara da Kaduna , aje dajin Kuzamani akan iyaka Kaduna da Neja”.

Sai dai kuma a dukkan wuraren nkamar yadda ya jaddada, “A dukkan wuraren akwai kungiya- kungiya ta ‘yan ta’adda wadanda suka kai muatane zuwa dazuzzukan,  ga shi kuma babu isassun jami’an tsaro a wuraren da suke da hatsari. Don haka akwai bukatar a shirya rundunar tsaro ta hadin gwiwa tskanin Jiha da Jiha a Jihohin, Kaduna, Neja da Zamfara.Abinda ya kamata ayi ke nan ba kawai a tsaya kan hanya ba ko kuma wasu wuraren al’umma .

Abinci
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
Abinci
Jibrin Baba Ndace
+ posts Bio
  • Jibrin Baba Ndace
    https://hausa.leadership.ng/author/jibrin-baba-ndace/
    Mohammed Idris Malagi A Ma’aunin Siyasa

MASU ALAKA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Next Post
GORON JUMA’A 22/11/2024

GORON JUMA'A 22/11/2024

LABARAI MASU NASABA

Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.