• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗaliba Ta Maka Makarantarsu A Kotu, Ta Nemi Diyyar Miliyan ₦505 Kan Cin Zarafinta

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
Kotu

Wata ɗalibar makarantar ‘Lead British International School’ da ke Gwarimpa a Abuja mai suna Namitra Bwala, ta kai ƙarar makarantarsu tare da neman a biya ta diyyar zunzurutun kuɗi har Naira Miliyan ₦505 sakamakon laifin cin zali da cin zarafin da aka yi mata.

Idan ba a manta ba LEADERSHIP HAUSA ta rawaito yadda lamarin ya afku bayan da wani faifan bidiyo ya watsu a shafukan sada zumunta wanda a bidiyon aka ga yadda wata ɗaliba mai suna Mariam Hassan take cin zalin Namtira Bwala, bidiyon dai ya janyo cece-ku-ce a kafafen sada zumunta, wanda hakan ya sa mutane da kungiyoyi suka yi tir da kuma kiran a yi mata adalci.

  • Ƙungiyar Ƙwadago Ta NLC Na Zanga-zanga Kan Ƙarin Ƙudin Wutar Lantarki A Nijeriya
  • NFF Za Ta Gabatar Da Finidi George A Matsayinl Sabon Kocin Super Eagles A Yau Litinin

Bayan faruwar hakan, mahukuntan makarantar sun fitar da wata sanarwa domin kwantar da hankula wacce take nuna za su yi bincike kan al’amarin.

Daga cikin waɗanda suka sanya baki a maganar har da ma’aikatar harkokin mata da kuma wacce ta aikata laifin wato Maryam inda ta fitar da wani bidiyon na bayar da haƙuri tare da neman afuwa.

Amma da alama wannan bai sanya iyalan Namitra Bwala su yafe ba. Domin kuwa a safiyar yau Litinin ne, Mista Daniel Madu Bwala, wanda yake a madadin mahaifinta ya shigar da makarantar ‘Lead British International School’ ƙara a wata babbar kotu da ke birnin tarayya Abuja bisa zarginsu da yin sakaci da rufa-rufar abinda ya faru.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kamfanin lauya mai wakiltar Namtira, Deji Adeyanju and Partners, sun bayyana cewa wanda suke wakiltar na son kotun ta tilastawa makarantar biyansu Naira miliyan ₦500m kuɗin diyya da kuma Naira miliyan biyar kuɗin da suka kashe wajen shari’a saboda sakacin makarantar na rashin ɗaukar matakan da ya dace kamar yadda doka ta tanada.

Bayan makarantar ta biya waɗannan miliyoyin kuɗaɗen, iyalan ɗalibar da aka muzanta na son a rubuta wasiƙar bayar da haƙuri gare su wacce dole sai an wallafa ta a manyan jaridu biyu na Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?
Manyan Labarai

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 
Manyan Labarai

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Manyan Labarai

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Next Post
Ƙungiyar Ƙwadago Ta NLC Na Zanga-zanga Kan Ƙarin Ƙudin Wutar Lantarki A Nijeriya

NLC Na Gudanar Da Zanga-zanga A Ofishin KEDCO Na Kano Kan Ƙarin Ƙuɗin Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

2023: Me Ya Sa Ake Rububin Wike?

Atiku Ya Fice Daga PDP Saboda Na Ƙi Bari Ya Lalata Mana Jam’iyya – Wike

November 4, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

Kalaman Trump A Kan Nijeriya Abun Damuwa Ne – Peter Obi 

November 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.