• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Ceto Ya Bayyana Ɗan Siyasar Da Ke Da Hannu Kan Kama Shi

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
10 months ago
in Labarai
0
Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Ceto Ya Bayyana Ɗan Siyasar Da Ke Da Hannu Kan Kama Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jim kaɗan bayan gudanar da Sallar jana’izar marigayi Sarkin Kudun Gatawa, Isa Muhammad Bawa ba tare da gawa ba wanda da ‘yan ta’adda suka yi wa kisan gilla, ɗan sa wanda aka kama su tare ya bayyana ɗan siyasar da ya ba wa ƴan ta’addan kwangilar yin garkuwa da Sarkin.

Ɗan Sarkin, Kabiru Isa wanda ‘yan ta’addan suka saki a daren jiya bayan biyan kudin fansar miliyan 60 da babura biyar ba tare da bayar da gawar basaraken ba, ya bayyana cewar Honarabul Aminu Boza ne ke da hannu wajen garkuwa da basaraken.

  • Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Kashe Ya Kuɓuta Daga Hannun ‘Yan Bindiga
  • Gwamnatin Sokoto Za Ta Sayar da Tireloli 300 Na Shinkafa A Farashi Mai Rahusa

An gudanar da Sallar jana’izar basaraken na Daular Gobir a safiyar yau a Kanwuri da ke Sabon- Birni a inda dubban al’umma suka halarta cike da jimami da bakin cikin kisan gillar da aka yi masa.

A wani bidiyon da aka ɗauke shi kan gadon asibiti na daƙiƙu 30, Kabiru wanda shi ne ke tuka Sarkin a mota yayin da aka kama su ya ce Honarabul Aminu Boza ne ‘yan ta’addan suka ce masu ya bayar da Naira miliyan biyar a kama Sarkin. Ya ce da shi da Sarkin duk sun bayyana masu hakan tare da cewar sun ce a ɗora masa tara.

Honarabul Aminu Boza shi ne Ɗan majalisar da ke wakiltar ƙaramar hukumar Sabon-Birni ta Arewa a majalisa dokokin Jihar Sakkwato a jam’iyyar APC ya kuma yi fice a baya wajen shiga kafafen yaɗa labarai yana suka da caccakar gwamnatin Aminu Waziri Tambuwal da ta gabata kan abin da ya kira kasawarta wajen kawar da matsalolin tsaro a Sabon- Birni da Gabacin Sakkwato baki ɗaya.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Dan majalisar wanda daga baya ya canza sheka daga PDP zuwa APC, ba a taba jin ya shiga kafafen yaɗa labarai ya soki gwamnatin Ahmed Aliyu kan ta’addancin da ‘yan bindigar ke yi ba kamar yadda ya yi a baya ba duk kuwa da ta’azzara da lamarin ya ƙara yi a yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BanditsGobirKidnappersPoliceTerrorist
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Ɗumi-ɗumi: Alƙalin Alƙalan Nijeriya,  Ariwoola Ya Yi Ritaya

Next Post

Majalisar Jihar Kebbi Ta Amince Da Ƙudirin Gyaran Dokar Ƙananan Hukumomi

Related

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

13 minutes ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

9 hours ago
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu
Labarai

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

11 hours ago
Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
Labarai

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

16 hours ago
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto
Labarai

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

18 hours ago
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo
Labarai

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

18 hours ago
Next Post
Majalisar Jihar Kebbi Ta Amince Da Ƙudirin Gyaran Dokar Ƙananan Hukumomi

Majalisar Jihar Kebbi Ta Amince Da Ƙudirin Gyaran Dokar Ƙananan Hukumomi

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.