• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Ceto Ya Bayyana Ɗan Siyasar Da Ke Da Hannu Kan Kama Shi

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
1 year ago
in Labarai
0
Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Ceto Ya Bayyana Ɗan Siyasar Da Ke Da Hannu Kan Kama Shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jim kaɗan bayan gudanar da Sallar jana’izar marigayi Sarkin Kudun Gatawa, Isa Muhammad Bawa ba tare da gawa ba wanda da ‘yan ta’adda suka yi wa kisan gilla, ɗan sa wanda aka kama su tare ya bayyana ɗan siyasar da ya ba wa ƴan ta’addan kwangilar yin garkuwa da Sarkin.

Ɗan Sarkin, Kabiru Isa wanda ‘yan ta’addan suka saki a daren jiya bayan biyan kudin fansar miliyan 60 da babura biyar ba tare da bayar da gawar basaraken ba, ya bayyana cewar Honarabul Aminu Boza ne ke da hannu wajen garkuwa da basaraken.

  • Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Kashe Ya Kuɓuta Daga Hannun ‘Yan Bindiga
  • Gwamnatin Sokoto Za Ta Sayar da Tireloli 300 Na Shinkafa A Farashi Mai Rahusa

An gudanar da Sallar jana’izar basaraken na Daular Gobir a safiyar yau a Kanwuri da ke Sabon- Birni a inda dubban al’umma suka halarta cike da jimami da bakin cikin kisan gillar da aka yi masa.

A wani bidiyon da aka ɗauke shi kan gadon asibiti na daƙiƙu 30, Kabiru wanda shi ne ke tuka Sarkin a mota yayin da aka kama su ya ce Honarabul Aminu Boza ne ‘yan ta’addan suka ce masu ya bayar da Naira miliyan biyar a kama Sarkin. Ya ce da shi da Sarkin duk sun bayyana masu hakan tare da cewar sun ce a ɗora masa tara.

Honarabul Aminu Boza shi ne Ɗan majalisar da ke wakiltar ƙaramar hukumar Sabon-Birni ta Arewa a majalisa dokokin Jihar Sakkwato a jam’iyyar APC ya kuma yi fice a baya wajen shiga kafafen yaɗa labarai yana suka da caccakar gwamnatin Aminu Waziri Tambuwal da ta gabata kan abin da ya kira kasawarta wajen kawar da matsalolin tsaro a Sabon- Birni da Gabacin Sakkwato baki ɗaya.

Labarai Masu Nasaba

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Dan majalisar wanda daga baya ya canza sheka daga PDP zuwa APC, ba a taba jin ya shiga kafafen yaɗa labarai ya soki gwamnatin Ahmed Aliyu kan ta’addancin da ‘yan bindigar ke yi ba kamar yadda ya yi a baya ba duk kuwa da ta’azzara da lamarin ya ƙara yi a yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BanditsGobirKidnappersPoliceTerrorist
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Ɗumi-ɗumi: Alƙalin Alƙalan Nijeriya,  Ariwoola Ya Yi Ritaya

Next Post

Majalisar Jihar Kebbi Ta Amince Da Ƙudirin Gyaran Dokar Ƙananan Hukumomi

Related

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

56 minutes ago
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

2 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

3 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

4 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

13 hours ago
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata
Labarai

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

13 hours ago
Next Post
Majalisar Jihar Kebbi Ta Amince Da Ƙudirin Gyaran Dokar Ƙananan Hukumomi

Majalisar Jihar Kebbi Ta Amince Da Ƙudirin Gyaran Dokar Ƙananan Hukumomi

LABARAI MASU NASABA

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

October 3, 2025
MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

MDD Ta Yi Alƙawarin Tallafa Wa Gidauniyar Malala Mai Rajin Inganta Ilimin ‘Ya’ya Mata

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

October 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.