• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Shekara 13 Ya Kashe Kansa Bayan Jami’an Tsaro Sun Azabtar Da shi

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Tsaro
0
Ɗan Shekara 13 Ya Kashe Kansa Bayan Jami’an Tsaro Sun Azabtar Da shi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani yaro mai shekaru 13 mai suna Wisdom Hashimu ya mutu ta hanyar rataye kansa a Unguwar Maigero da ke Karamar Hukumar Chikun a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne bayan wani soja da jami’an rundunar hadin gwiwa ta Cibilian Task Force a yankin sun azabtar da marigayin.

  • Sojoji Sun Kashe Boko Haram 4 A Borno
  • Boko Haram Sun Sace Fasinjoji A Kan Hanyar Maiduguri Zuwa Kano

Marigayi Wisdom wadda ta aikata wannan aika-aika a harabar gidan da ke kan titin Lafiya Sarki an ce an zarge shi da laifin satar Naira 10,000 daga wata makwabciyarsu a ranar.

A wani rahoto da gidan Talabijin na Channels TB ta fitar, makwabciyarta mai shekaru 16 mai suna Hope, an ce ta gayyaci saurayinta mai suna Segun Samson, wanda soja ne a sansanin Bodi da ke Fatakwal, babban birnin jihar Ribers wanda ya shiga cikin maganar.

Sai dai an nemi kudi an rasa a lokacin ziyarar, wanda hakan ya sa Hope ta hada saurayin nata da Wisdom da kuma dan uwanta zuwa ofishin Cibilian JTF.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

Wisdom wacce ke zana jarabawar Karamar Sakandare, an bayyana cewa wani soja da jami’an Cibilian JTF ne suka yi masa mugun duka.

Mahaifin Wisdom, Mista Saul, wanda ya zanta da manema labarai ya ce, “Maimakon su kai rahoto ga ‘yansanda, sai kawai sojan ya ja dan’uwan Wisdom da Hope, wadanda ake zargi da satar kudin zuwa ofishin cibilian JTF.

“A ofishin cibilian JTF, an yi wa Wisdom mugun duka har ya kasa tafiya. Ya koma gida inda aka fara kula da lafiyarsa.”

Sai dai kuma wani abin takaici da ya afku shi ne an tsinci gawar Wisdom ya rataye kansa a bayan gidansu.

Sai dai a yayin da yake magana cikin bacin rai, mahaifin ya ce ‘yan Cibilian JTF sun dauki doka a hannunsu ta hanyar azabtar da Wisdom.

“Amma, ni abin da tunanina ya bani, Cibilian JTF ne kawai suka lakada wa Wisdom duka har ta kai ga suma, yayin da kanin Hope ya tsira ya dawo gida.

“Bayan an yi mata tambayoyi a gida, kaninta Hope ya amsa laifin da ya aikata, bayan da aka gano Naira 9,000 a aljihunsa, ya ce ya riga ya kashe Naira 1,000,” a cewarsa.

Don haka dangin sun bukaci a yi adalci kan azabtarwa da ake zargin marigayi dansu wanda hakan ya kai ga kashe shi.

“Tun daga lokacin aka fara bincike. Kwamishinan ‘yansandan ya umarci sashen binciken manyan laifuka da ya dauki nauyin lamarin kuma duk wanda ke da hannu za a gurfanar da shi a gaban kotu domin tabbatar da adalci”

Wisdom da ke zana jarabawar karamar Sakandare, an bayyana cewa wani soja da jami’an Cibilian JTF ne suka yi masa mugun duka.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, Mansir Hassan, ya ce an fara bincike kan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramBornoCJTFMaiduguriTsaroZulum
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping: Ba Zan Ci Amanar Jama’a Ba

Next Post

Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

Related

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

18 hours ago
Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina
Tsaro

Bayan Sulhu  Da Ƴan Bindiga, An Saki Mutane 70 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina

2 weeks ago
Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya
Tsaro

Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya

2 weeks ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

3 weeks ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

3 weeks ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi
Tsaro

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

4 weeks ago
Next Post
Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.