ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikin Mako 2, An Kashe Jami’an Tsaro 53 A Faɗin Nijeriya

by Abubakar Sulaiman
12 months ago
Tsaro

A ƙalla jami’an tsaro 53 aka kashe a faɗin Najeriya cikin makonni biyu da suka gabata, bisa ga ƙididdigar da Daily Trust ta tattara daga rahotannin kafafen watsa labarai. Waɗanda aka kashe sun haɗa da Sojoji, da ƴansanda, da jami’an NSCDC, da na shige-da-fice da na haraji, da kuma na sa-kai, da mambobin JTF da ƙungiyoyin tsaron al’umma na jihohi. Wannan adadi bai haɗa da rahotannin da ba a bayar ba.

Yawancin jami’an an kashe su ne yayin da suke amsa kiran kai hari kan al’umma, yayin da wasu kuma aka yi musu kwanton ɓauna a wuraren binciken ababen hawa da sansanonin tsaro. Manyan hare-haren kwanan nan sun faru ne a jihohin Biniwe da Kogi, inda ƴan bindiga suka hallaka jami’an ƴansanda bakwai da wasu jami’an tsaro a hare-hare dabam-dabam tsakanin Juma’a da Lahadi. Haka kuma an yi garkuwa da wasu jami’an a lamarin da ya auku a Binuwe

  • Ƴan Bindiga Sun Yi Wa 9 NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
  • Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Waɗannan kashe-kashen sun ƙara haskaka yadda barazanar tsaro ke ta ƙara jawo asarar rayukan jami’an tsaro a Nijeriya. Binciken da Daily Trust ta gudanar a watan Disambar 2024 ya nuna cewa an kashe a ƙalla ƴan sanda 229 daga Janairu 2023 zuwa Oktoba 2024 sakamakon hare-haren ƴan bindiga, da na masu tada kayar baya, masu al’ada da kuma ƴan fashi da makami. Sabbin hare-haren sun nuna cewa tashin hankali na ƙaruwa duk da yunƙurin samar da tsaro da ake ci gaba da gudanarwa.

ADVERTISEMENT

A martanin Hukumar DSS, ta gurfanar da mutane tara a gaban Babbar Kotun Tarayya a Abuja a makon jiya kan zargin hannu a kisan da aka yi kwanan nan a jihohin Binuwe da Filato. Cikin waɗanda aka gurfanar har da Haruna Adamu da Muhammad Abdullahi daga Jihar Nasarawa, bisa zargin hannu a kisan gilla da aka yi a Guma LGA ta Benue.

Haka kuma an gurfanar da Terkende Ashuwa da Amos Alede bisa zargin ramuwar gayya da ta haddasa lalata kadarori da rasa shanu 12 a ƙauyen Ukpam. DSS ta kuma gurfanar da wani mutum daban kan mallakar bindigogi M16 guda bakwai ba bisa ƙa’ida ba.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Tsaro
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote
  • Abubakar Sulaiman
    Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Sace Basarake Da Mata 2 A Filato

Ƴan Bindiga Sun Sace Basarake Da Mata 2 A Filato

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.