• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Takarar Gwamnan NNPP A Katsina Zai Kawar Da Ƙazantar APC Da PDP – Hajiya Farida Barau

by yahuzajere
3 years ago
in Siyasa
0
Ɗan Takarar Gwamnan NNPP A Katsina Zai Kawar Da Ƙazantar APC Da PDP – Hajiya Farida Barau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan ɗan takarar Gwamnan Jihar Katsina a Jam’iyyar NNPP, Engr Nura Khalil, wato Hajiya Farida Muhammad Barau ta bayyana cewa duk mutanen da ke cikin jam’iyyar NNPP mutanen kirki ne da ba su taɓa ɗaukar alhakin kowa a siyasa ba.

Uwargidan ɗan takarar rar ta bayyana hakan ne a ofishin yaƙin neman zaɓen maigidan nata da ke kan titin IBB Way cikin birnin Katsina, lokacin da ta ƙaddamar da muhimman manufofin takararsa ga matan jihar Katsina.

Hajiya Farida Muhammad Barau ta yi bayanin cewa ce; “Lema ta yage, tsintsiya ta watse, an ɗora mana yunwar dole, an sa mana talauci, mai cin abinci sau uku yanzun ma babu, an maida mu jawarawa, an kashe mana mazajenmu, an sace mana mata, shin wai haka za mu zauna ne?

“Mun zama shanaye an maida mu awakai, wannan Jam’iyya ta NNPP jaririya ce ba ta da hakkin kowa wallahi, mutanen duk da kuka gani cikin wannan jam’iyar mutanen kirki ne. Engr Muhammad Nura Khalil ya daɗe yana taimako, mai tausayi ne da kuɗinsa yake amfani yake fiddawa ya ba da, bai taɓa riƙe ko kansila ba, amma ya san hanyar da ake neman kuɗi, kuma a cikinsa yake ɗiba yake taimakon mutane.

“Shin ina ga ya samu wata dama wadda zai taimake ku da kuɗinku? Mine ne ba zai maku ba? Bai iya cin haƙƙin mutane ba, bai taɓa aikin gwamnati ba, bai taɓa ciyar da iyalinsa da haramun ba, bugu da ƙari ga shi yana da tausayin mata da ƙananan yara da matasa.” In ji Hajiya Farida.

Labarai Masu Nasaba

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

  • Da Dumi-dumi: Gwamnan Gombe Ya Rushe Shugabannin Kananan Hukumomin Bayan Karewar Wa’adin Mulkinsu

Har ila yau, shi ma a nasa jawabin, ɗan takarar gwamnan na NNPP a Jihar Katsina, Engr Muhammad Nura Khalil ya bayyana cewa idan ya lashe zaɓen jihar matan Katsina za su ji daɗi sosai, inda ya ƙara da cewa duk wata sai ya tallafi matan jihar Katsina dubu talatin da huɗu da kayan tallafi kuma har ya kammala wa’adinsa ba zai daina ba.

NNPP

Haka zalika da yake tofa albarkacin bakinsa, shugaban jam’iyyar NNPP ta Jihar katsina Honorable Sani Liti Yankwani ya yaba ma uwargidan dantakarar gwamnan a bisa ƙoƙarin da take na ganin maigidanta ya samu nasara da ma jam’iyya baki ɗaya, a zaɓe mai zuwa na 2023.

Ya ƙara da cewa babu shakka duk inda ka ga namiji ya samu nasara to za ka same shi da mace irin Hajiya Farida Muhammad Barau a tare da shi domin ita mace ce mai nagarta da kuma sanin ya kamata, “kazalika idan ba ka zauna da Farida ba ba za ka san wace ce Farida ba domin mace ce mai son ganin ci gaban Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya.”
Shi ma a nasa jawabin, Kwamrad Bashir Bala Funtua, ɗaya daga cikin matasan da ke dafa wa ɗan takarar na NNPP, Engr Nura Khalil baya wajen fafutukar jawo matasa don mara masa, ya bayyana cewa “ka da wata mace a Jihar Katsina ta yarda wasu ‘yan siyasa su ba su ‘yan kudi ƙalilan don zaɓar su, su tsaya su dubi cancanta su mara wa Engr Nura Khalil baya don samun kyakkyawan shugabanci a jihar Katsina.” In ji shi

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kungiyoyin Cinikayya Na Sin Sun Tafi Waje Don Neman Jari

Next Post

Yarjejeniyar Kare Mabambanta Hallitu a Duniya Ta Kunming Da Montreal Ta Fidda Wata Hanya Mai Dacewa a Fannin Kare Hallitu

Related

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

5 hours ago
Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100

3 days ago
Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
Siyasa

Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 

3 days ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

3 days ago
Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
Manyan Labarai

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

3 days ago
Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna
Siyasa

Mutumin El-Rufai, Baloni, Ya Fice Daga APC A Kaduna

4 days ago
Next Post
Yarjejeniyar Kare Mabambanta Hallitu a Duniya Ta Kunming Da Montreal Ta Fidda Wata Hanya Mai Dacewa a Fannin Kare Hallitu

Yarjejeniyar Kare Mabambanta Hallitu a Duniya Ta Kunming Da Montreal Ta Fidda Wata Hanya Mai Dacewa a Fannin Kare Hallitu

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

July 25, 2025
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

July 25, 2025
Amcon

Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi

July 25, 2025
Jiragen NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Lalata Baburansu 40 Da Bindigu 6 A Borno

Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

July 25, 2025

Bukatar Hukunta Masu Jagorantar Kashe-kashe A Nijeriya

July 25, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tura Dakarunta Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Yankin Olle-Bunu Na Jihar Kogi

July 25, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Hukumar ‘Yansanda Ta Yi Wa Wasu Manyan Jami’anta Karin Girma

July 25, 2025
Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa

July 25, 2025
Wutar lantarki

Arewa Maso Gabas Ce Za Ta Biya Kudin Wuta Mafi Tsada A Sabon Tsarin Lantarki

July 25, 2025
Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

Gwamna Lawal Ya Yi Ta’aziyyar Sarkin Katsinan Gusau

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.