ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Takarar Gwamnan NNPP A Katsina Zai Kawar Da Ƙazantar APC Da PDP – Hajiya Farida Barau

by yahuzajere
3 years ago
nnpp

Uwargidan ɗan takarar Gwamnan Jihar Katsina a Jam’iyyar NNPP, Engr Nura Khalil, wato Hajiya Farida Muhammad Barau ta bayyana cewa duk mutanen da ke cikin jam’iyyar NNPP mutanen kirki ne da ba su taɓa ɗaukar alhakin kowa a siyasa ba.

Uwargidan ɗan takarar rar ta bayyana hakan ne a ofishin yaƙin neman zaɓen maigidan nata da ke kan titin IBB Way cikin birnin Katsina, lokacin da ta ƙaddamar da muhimman manufofin takararsa ga matan jihar Katsina.

Hajiya Farida Muhammad Barau ta yi bayanin cewa ce; “Lema ta yage, tsintsiya ta watse, an ɗora mana yunwar dole, an sa mana talauci, mai cin abinci sau uku yanzun ma babu, an maida mu jawarawa, an kashe mana mazajenmu, an sace mana mata, shin wai haka za mu zauna ne?

ADVERTISEMENT

“Mun zama shanaye an maida mu awakai, wannan Jam’iyya ta NNPP jaririya ce ba ta da hakkin kowa wallahi, mutanen duk da kuka gani cikin wannan jam’iyar mutanen kirki ne. Engr Muhammad Nura Khalil ya daɗe yana taimako, mai tausayi ne da kuɗinsa yake amfani yake fiddawa ya ba da, bai taɓa riƙe ko kansila ba, amma ya san hanyar da ake neman kuɗi, kuma a cikinsa yake ɗiba yake taimakon mutane.

“Shin ina ga ya samu wata dama wadda zai taimake ku da kuɗinku? Mine ne ba zai maku ba? Bai iya cin haƙƙin mutane ba, bai taɓa aikin gwamnati ba, bai taɓa ciyar da iyalinsa da haramun ba, bugu da ƙari ga shi yana da tausayin mata da ƙananan yara da matasa.” In ji Hajiya Farida.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

  • Da Dumi-dumi: Gwamnan Gombe Ya Rushe Shugabannin Kananan Hukumomin Bayan Karewar Wa’adin Mulkinsu

Har ila yau, shi ma a nasa jawabin, ɗan takarar gwamnan na NNPP a Jihar Katsina, Engr Muhammad Nura Khalil ya bayyana cewa idan ya lashe zaɓen jihar matan Katsina za su ji daɗi sosai, inda ya ƙara da cewa duk wata sai ya tallafi matan jihar Katsina dubu talatin da huɗu da kayan tallafi kuma har ya kammala wa’adinsa ba zai daina ba.

NNPP

Haka zalika da yake tofa albarkacin bakinsa, shugaban jam’iyyar NNPP ta Jihar katsina Honorable Sani Liti Yankwani ya yaba ma uwargidan dantakarar gwamnan a bisa ƙoƙarin da take na ganin maigidanta ya samu nasara da ma jam’iyya baki ɗaya, a zaɓe mai zuwa na 2023.

Ya ƙara da cewa babu shakka duk inda ka ga namiji ya samu nasara to za ka same shi da mace irin Hajiya Farida Muhammad Barau a tare da shi domin ita mace ce mai nagarta da kuma sanin ya kamata, “kazalika idan ba ka zauna da Farida ba ba za ka san wace ce Farida ba domin mace ce mai son ganin ci gaban Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya.”
Shi ma a nasa jawabin, Kwamrad Bashir Bala Funtua, ɗaya daga cikin matasan da ke dafa wa ɗan takarar na NNPP, Engr Nura Khalil baya wajen fafutukar jawo matasa don mara masa, ya bayyana cewa “ka da wata mace a Jihar Katsina ta yarda wasu ‘yan siyasa su ba su ‘yan kudi ƙalilan don zaɓar su, su tsaya su dubi cancanta su mara wa Engr Nura Khalil baya don samun kyakkyawan shugabanci a jihar Katsina.” In ji shi

 

nnpp
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Yarjejeniyar Kare Mabambanta Hallitu a Duniya Ta Kunming Da Montreal Ta Fidda Wata Hanya Mai Dacewa a Fannin Kare Hallitu

Yarjejeniyar Kare Mabambanta Hallitu a Duniya Ta Kunming Da Montreal Ta Fidda Wata Hanya Mai Dacewa a Fannin Kare Hallitu

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.