ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan Takarar Gwamnan NNPP A Katsina Zai Kawar Da Ƙazantar APC Da PDP – Hajiya Farida Barau

by yahuzajere
4 years ago
nnpp

Uwargidan ɗan takarar Gwamnan Jihar Katsina a Jam’iyyar NNPP, Engr Nura Khalil, wato Hajiya Farida Muhammad Barau ta bayyana cewa duk mutanen da ke cikin jam’iyyar NNPP mutanen kirki ne da ba su taɓa ɗaukar alhakin kowa a siyasa ba.

Uwargidan ɗan takarar rar ta bayyana hakan ne a ofishin yaƙin neman zaɓen maigidan nata da ke kan titin IBB Way cikin birnin Katsina, lokacin da ta ƙaddamar da muhimman manufofin takararsa ga matan jihar Katsina.

Hajiya Farida Muhammad Barau ta yi bayanin cewa ce; “Lema ta yage, tsintsiya ta watse, an ɗora mana yunwar dole, an sa mana talauci, mai cin abinci sau uku yanzun ma babu, an maida mu jawarawa, an kashe mana mazajenmu, an sace mana mata, shin wai haka za mu zauna ne?

ADVERTISEMENT

“Mun zama shanaye an maida mu awakai, wannan Jam’iyya ta NNPP jaririya ce ba ta da hakkin kowa wallahi, mutanen duk da kuka gani cikin wannan jam’iyar mutanen kirki ne. Engr Muhammad Nura Khalil ya daɗe yana taimako, mai tausayi ne da kuɗinsa yake amfani yake fiddawa ya ba da, bai taɓa riƙe ko kansila ba, amma ya san hanyar da ake neman kuɗi, kuma a cikinsa yake ɗiba yake taimakon mutane.

“Shin ina ga ya samu wata dama wadda zai taimake ku da kuɗinku? Mine ne ba zai maku ba? Bai iya cin haƙƙin mutane ba, bai taɓa aikin gwamnati ba, bai taɓa ciyar da iyalinsa da haramun ba, bugu da ƙari ga shi yana da tausayin mata da ƙananan yara da matasa.” In ji Hajiya Farida.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

  • Da Dumi-dumi: Gwamnan Gombe Ya Rushe Shugabannin Kananan Hukumomin Bayan Karewar Wa’adin Mulkinsu

Har ila yau, shi ma a nasa jawabin, ɗan takarar gwamnan na NNPP a Jihar Katsina, Engr Muhammad Nura Khalil ya bayyana cewa idan ya lashe zaɓen jihar matan Katsina za su ji daɗi sosai, inda ya ƙara da cewa duk wata sai ya tallafi matan jihar Katsina dubu talatin da huɗu da kayan tallafi kuma har ya kammala wa’adinsa ba zai daina ba.

NNPP

Haka zalika da yake tofa albarkacin bakinsa, shugaban jam’iyyar NNPP ta Jihar katsina Honorable Sani Liti Yankwani ya yaba ma uwargidan dantakarar gwamnan a bisa ƙoƙarin da take na ganin maigidanta ya samu nasara da ma jam’iyya baki ɗaya, a zaɓe mai zuwa na 2023.

Ya ƙara da cewa babu shakka duk inda ka ga namiji ya samu nasara to za ka same shi da mace irin Hajiya Farida Muhammad Barau a tare da shi domin ita mace ce mai nagarta da kuma sanin ya kamata, “kazalika idan ba ka zauna da Farida ba ba za ka san wace ce Farida ba domin mace ce mai son ganin ci gaban Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya.”
Shi ma a nasa jawabin, Kwamrad Bashir Bala Funtua, ɗaya daga cikin matasan da ke dafa wa ɗan takarar na NNPP, Engr Nura Khalil baya wajen fafutukar jawo matasa don mara masa, ya bayyana cewa “ka da wata mace a Jihar Katsina ta yarda wasu ‘yan siyasa su ba su ‘yan kudi ƙalilan don zaɓar su, su tsaya su dubi cancanta su mara wa Engr Nura Khalil baya don samun kyakkyawan shugabanci a jihar Katsina.” In ji shi

 

nnpp
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Yarjejeniyar Kare Mabambanta Hallitu a Duniya Ta Kunming Da Montreal Ta Fidda Wata Hanya Mai Dacewa a Fannin Kare Hallitu

Yarjejeniyar Kare Mabambanta Hallitu a Duniya Ta Kunming Da Montreal Ta Fidda Wata Hanya Mai Dacewa a Fannin Kare Hallitu

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.