ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 weeks ago
Idanu

Wani matashi mai suna Auwalu Muhammad ya kwaƙule idanuwan ƙannuwarsa ‘yar shekara bakwai a duniya, Rukayya Muhammad, domin yin tsafin neman kuɗi a yunƙurinsa na zama hamshaƙin mai kuɗi. 

Wannan dai na zuwa ne bayan da Boka mai bayar da sa’ar yin kuɗi da ke sanya jama’a ciro sassan jikin mutane kamar idanu da azzakari ya nemi Auwalu da ya ciro idanun yarinyar domin a masa tsafi ya zama mai kuɗi dare guda. 

  • Don Nuna Wa Duniya Kyawawan Al’adunmu Na Kirkiri Manhajar ‘Unlock Arewa’ – Bappi
  • Don Nuna Wa Duniya Kyawawan Al’adunmu Na Kirkiri Manhajar ‘Unlock Arewa’ – Bappi

A halin yanzu likita ya tabbatar da cewar Rukayya ba za ta sake gani ba domin idanuwanta sun lalace gaba ɗaya. 

ADVERTISEMENT

Wannan abun takaici ya faru ne a yankin Wailo da ke ƙaramar hukumar Ganjuwa a jihar Bauchi.

A lokacin da ake zantawa da mahaifin yarinyar ya bayyana cewar wanda ake zargin (Auwalu) ya yaudari ‘yar uwar tasa, wacce suke da iyaye guda tare, zuwa daji tare da kwaƙule mata idanu da ƙarfin tsiya. 

LABARAI MASU NASABA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

Mahaifin Rukayya, Muhammad Adamu mazaunin ƙauyen Bayan Dutse da ke Wailo, a gundumar Kubi cikin ƙaramar hukumar Ganjuwa a ranar 17 ga watan Oktoba ya kai rahoton caji ofis ɗin Soro ya ke shaida cewar wani matashi mai suna Auwal Dahiru mai shekara 17, ya kai farmaƙi wa yarsa da ƙoƙarin kasheta da kwaƙule mata idanuwanta. 

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, CSP Ahmed Mohammed Wakil a ranar Litinin, ya ce, lokacin da ‘yansanda suka samu rahoton faruwar lamarin cikin gaggawa a ƙarƙashin Baturen ɗansanda da ke kula da caji ofis ɗin Soro, CSP Aliyu Mohammad Goni, sun kai agaji inda lamarin ya faru.

A lokacin da aka ɗauki Rukayya zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBUTH), Bauchi, domin mata jinya, kwararren likitan Ido a asibitin ya tabbatar da cewar yarinyar ba za ta sake gani da idanuwanta ba har ƙarshen rayuwarta. 

Kan haka ne rundunar ‘yansandan ta ce zuwa yanzu ta cafke mutane shida da ake zargi da hannu kan wannan aika-aikar waɗanda suka haɗa da Auwal Dahiru, mai shekara 17 da ke Bayan Dutse, Wailo, Kubi, Ganjuwa, Mohammed Rabiu (mai shekaru 19), Saleh Ibrahim (20), Nasiru Muhammad mazaunin cikin garin Soro a Ganjuwa, Hassan Garba mazaunin Soro da kuma Garba Dahiru mai shekara 43 a duniya kuma mazaunin Soro.

“Lokacin da ake bincike, waɗanda ake zargin sun amsa laifinsu,” Wakil ya tabbatar.

Jami’in watsa labaran ‘yansandan ya kuma sanar da cewa yanzu haka bincike na ci gaba da gudana domin zaƙulo dukkanin masu hannu a wannan aikin domin su fuskanci Shari’a. 

Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi,  State Command, CP Sani-Omolori Aliyu, ya umarci a gaggauta maida binciken kes ɗin zuwa sashin binciken manyan laifukan (SCID), Bauchi domin faɗaɗa bincike da gano wasu abubuwan da suke akwai kan lamarin. 

Ya bayar da tabbacin wanzar da gaskiya da adalci kan lamarin da yin aiki bisa kwarewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna
Labarai

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2
Manyan Labarai

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
Next Post
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.