ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Don Nuna Wa Duniya Kyawawan Al’adunmu Na Kirkiri Manhajar ‘Unlock Arewa’ – Bappi

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
arewa

Wani matsashi haifaffen Jihar Gombe kuma kwararre a bangaren fasanhohin zamani, Nasir Bappi, ya kirkiri sabuwar manhajar ‘Unlock Arewa’ a yanar gizo.

Ya ce ya kirkiri manhajar ne don nuna wa duniya kyayawan al’adun Hausawa na gargajiya.

  • Ƙarancin Wayewa da Samar Da Labaru Masu Kyau Ke Durƙusar Da Kannywood
  • Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya(2)

Matashin ya ce ya bude manhajar ne don saukaka wa mutane wajen musayar fasahohi tare da habaka kasuwanci tsakanin juna, gami da kokarinsa na fito sa kyawawan al’adun gargajiya da suke arewa ga duniya baki daya.

ADVERTISEMENT

Manhajar ta kunshi al’adun Hausawa har da abin da ya shafi masarautu da sutura da abinci da sauran abubuwan al’adar Malam Bahaushe. Sabuwar manhajar na dauke da al’adun garuruwan Hausawa daban-daban da ire-iren abincin da aka fi ci a wadannan garuruwa.

Ya ce babban burinsa shi ne taimaka wa mutane wajen yada kasuwancisu ta hanyar manhajar
Ya ce, “Na kirkiri manhajar ‘Unlock Arewa’ domin ya taimaka wa mutanenmu da suke arewacin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Yadda na tsinci kaina a wannan fasahar shi ne lokacin da nake karatu a kasan waje bayan na karanci darasin ‘information technology’, bayan da na dawo Nijeriya shi ne na zo na bude kamfani mai suna ‘Unlock Arewa’.

“Dalilin da ya sa muka bude wannan manhajar shi ne mu saukaka wa mutane wajen musayan ra’ayoyi da abubuwa da yadda kuma matane suke kasuwanci, sannan da bunkasa al’adunmu da tarihinmu da abubuwan da suka kamata.

“Akwai masarautunmu da sarakunanmu, za ka ga yadda mutane ke cin abinci da yadda suke abubuwa, don haka a wannan manhajar mun yi kokarin kawo duk wadannan abubuwan domin sannu a hankali muna kokarin mantawa da al’adunmu da tarihinmu.

“Babban burina na bude wannan manhajar shi ne na taimaka wa mutane su samu ayyuka ta wannan manhajar da yadda za su ke tattaunawa da juna bayan haka kar su manta da al’adunsu ta hanyar suke karantawa domin sanin abubuwan da ke faruwa da wadanda suka faru.

“Babu yadda za a yi mu ci gaba ba tare da mun san bayanmu ba. Don haka muna bi gari-gari, kauye-kauye muna koyar da mutane kyauta.”

Ya ce a kalla zuwa yanzu sun koyar da mutane kusan 6,800 domin su kara samun ilimi na fasahar zamani kuma su taimaka wa kansu, “Daga gida mace za ta iya aikinta ta samu kudade ko na miji ya yi aikinsa daga gida ya samu kudadensa ba tare da a dogara da gwamnati ba.

“A cikin manhajar namu mutum idan ya duba zai ga kowace gari akwai masarautu daban-daban. Ni yanzu misali a ce ni dan Gombe ne ban san Masarautun Kano ba, ban san yadda suke al’adunsu ba, ban san wani irin abinci suke ci ba, sai dai kawai a ce Hausa /Fulani.

“To daga ka shiga ciki za ka ga kowace masarauta da yadda suke suna, yadda suke aure, yadda suke rayuwarsu, wasu irin sana’o’i suke yi, mutanen da suke harkar kiwon ne ko saka ne, ko me ye za ka samu a wannan manhajar.

“Muna son mu sanya arewa a tafin hannun mutane mu daukakata da al’adunta.

“Manhajar Unlock Arewa a yanzu muna da masu wakiltarmu a kasashe 32 wadanda suna taimaka wa matane kama daga neman guraben karatu, tallafin karatu, kasuwanci, misali kana son sayan kaya a China ba ka san waye za ka dogara da shi ba, shi wakilinmu zai taimaka maka hada da masu sayarwa har kayanka ya zo Nijeriya.

“Bayan haka kuma, a kowace kasa in kana bukatar abu ko in za ka je yawan bude ido ko wani abu za su taimaka maka su hada da kamfanin da ya kamata wanda ba za a cuceka ba kuma su maka bayanin abubuwan da za su taimakeka a wannan kasar.

“Na kirkiri wannan manhajar saboda in nuna wa duniya kyawawan al’adunmu na gargajiya. Babban burina shi ne in hada arewa da duniya ta yadda za mu taimaka wa juna gabaki daya.”

arewa
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
arewa
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Zarewa Ta Ƙirƙiro Na’urar Gano Tsatsa Bayan Lashe Kyautar ‘Carbon Neutrality’ Ta Duniya

February 21, 2026
Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Next Post
mbappe

Ba Na Jin Dadin Saka Abin Kariyar Fuska, Cewar Mbappe

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.