• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Da BVAS Da IReV Za Mu Yi Amfani Wajen Tattara Sakamakon Zabe – INEC

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daidai ya rage saura kwanaki 100 a yi zaɓen shugaban ƙasa, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta jaddada cewa ba za ta taɓa fasa bin sabon tsarin ta na tattara sakamakon zaɓe da tantance yawan ƙuri’u na BVAS da IReV ba, domin tabbatar da sahihin zaɓe.

Shugaban INEC Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka, cikin wata sanarwar da hukumar ta fitar a ranar Laraba, inda ya ce an bijiro da tsarin amfani da BVAS da IReV ne domin hana murɗiya, maguɗi da satar akwati lokacin gudanar da zaɓen 2023.

  • 2023: INEC Ta Nemi Masu Kada Kuri’a Da Su Duba Sunayensu Cikin Wadanda Ta Yi Wa Rajista

Yakubu ya yi wannan ƙarin haske ranar Laraba, cikin jawabin da ya fitar daidai saura kwanaki 100 cif kafin a yi zaɓen shugaban ƙasa da na Majalisar Tarayya, wanda za a yi ranar 25 Ga Fabrairu 2023.

Za a gudanar da zaɓen gwamnoni da na Majalisar Dokoki a ranar 11 Ga Maris, makonni biyu bayan zaɓen gwamna.

Kwanan nan wasu masu katsalandan sun yi ƙoƙarin kiran INEC da ta janye shirin yin amfani da na’urorin BVAS da IReV wajen tantance masu jefa ƙuri’a a lokacin da za a kaɗa ƙuri’u a zaɓen 2023.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Masu neman kada a yi amfani da BVAS da IReV sun ce gara a koma yin amfani da fallen takarda, wato fam wanda za a riƙa rubuta adadin ƙuri’un da kowane ɗan takara ko jam’iyya ta samu.

INEC ta daina amfani da wancan tsohon tsarin rubuta sakamako a fallayen takardu tun bayan ƙirƙiro tsarin BVAS da IReV, wanda ta ce da shi za ta yi amfani a zaɓen 2023.

A kan haka ne Yakubu ya ce tuni an shirya yin amfani da sabon tsarin a zaɓe mai zuwa, kuma ba za a fasa yin amfani da tsarin ba.

“Kamar yadda na sha nanatawa, INEC Nijeriya ta ke yi wa aiki, ba wata jam’iyya ko wani ɗan siyasa ba. ‘Yan Nijeriya mu ke wa aiki tare sadaukarwa. Saboda jama’a buƙatar sahihin zaɓe mai inganci, wanda zai zama karɓaɓɓe ta hanyar amfani da tsarin na’rorin fasaha, waɗanda za su tabbatar da cewa an yi bi sahihiyar hanyar tantance masu rajistar shaidar masu jefa ƙuri’a. Daga nan kuma za a loda sakamakon kai-tsaye daga rumfukan zaɓe zuwa shafukan rariyar tattara bayanan INEC, yadda kowa zai iya shiga ya duba sakamakon zaɓe tun a ranar da aka kaɗa ƙuri’a.

“Saboda haka dalili kenan aka ƙirƙiro BVAS da IReV. Kuma ba za mu fasa yin amfani da waɗannan tsare-tsare guda biyu ba a zaɓen 2023,” inji Yakubu.

Shugaban na INEC ya ce nan da makonni kaɗan hukumar sa za ta fara yin taron ganawa da manema labarai duk bayan sati biyu, domin ta riƙa sanar wa ‘yan Najeriya irin shirin da ta ke ciki dangane da tunkarar zaɓen 2023.

Ya ce idan zaɓen ya kusa ne INEC za ta riƙa yin taron zantawa da manema labarai a kowace rana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gasar Kofin Kwallon Kafa 2022: Qatar Ta Haramta Hadadar Barasa A Filayen Wasanninta

Next Post

Kotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Zargin Damfarar N544m

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

1 hour ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

4 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

15 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

21 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

22 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

23 hours ago
Next Post
Kotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Zargin Damfarar N544m

Kotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Zargin Damfarar N544m

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.