• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Da BVAS Da IReV Za Mu Yi Amfani Wajen Tattara Sakamakon Zabe – INEC

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Kona Ofishin Zabe: INEC Ta Kira Taron Gaggawa Da Hukumomi Tsaro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daidai ya rage saura kwanaki 100 a yi zaɓen shugaban ƙasa, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta jaddada cewa ba za ta taɓa fasa bin sabon tsarin ta na tattara sakamakon zaɓe da tantance yawan ƙuri’u na BVAS da IReV ba, domin tabbatar da sahihin zaɓe.

Shugaban INEC Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka, cikin wata sanarwar da hukumar ta fitar a ranar Laraba, inda ya ce an bijiro da tsarin amfani da BVAS da IReV ne domin hana murɗiya, maguɗi da satar akwati lokacin gudanar da zaɓen 2023.

  • 2023: INEC Ta Nemi Masu Kada Kuri’a Da Su Duba Sunayensu Cikin Wadanda Ta Yi Wa Rajista

Yakubu ya yi wannan ƙarin haske ranar Laraba, cikin jawabin da ya fitar daidai saura kwanaki 100 cif kafin a yi zaɓen shugaban ƙasa da na Majalisar Tarayya, wanda za a yi ranar 25 Ga Fabrairu 2023.

Za a gudanar da zaɓen gwamnoni da na Majalisar Dokoki a ranar 11 Ga Maris, makonni biyu bayan zaɓen gwamna.

Kwanan nan wasu masu katsalandan sun yi ƙoƙarin kiran INEC da ta janye shirin yin amfani da na’urorin BVAS da IReV wajen tantance masu jefa ƙuri’a a lokacin da za a kaɗa ƙuri’u a zaɓen 2023.

Labarai Masu Nasaba

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Masu neman kada a yi amfani da BVAS da IReV sun ce gara a koma yin amfani da fallen takarda, wato fam wanda za a riƙa rubuta adadin ƙuri’un da kowane ɗan takara ko jam’iyya ta samu.

INEC ta daina amfani da wancan tsohon tsarin rubuta sakamako a fallayen takardu tun bayan ƙirƙiro tsarin BVAS da IReV, wanda ta ce da shi za ta yi amfani a zaɓen 2023.

A kan haka ne Yakubu ya ce tuni an shirya yin amfani da sabon tsarin a zaɓe mai zuwa, kuma ba za a fasa yin amfani da tsarin ba.

“Kamar yadda na sha nanatawa, INEC Nijeriya ta ke yi wa aiki, ba wata jam’iyya ko wani ɗan siyasa ba. ‘Yan Nijeriya mu ke wa aiki tare sadaukarwa. Saboda jama’a buƙatar sahihin zaɓe mai inganci, wanda zai zama karɓaɓɓe ta hanyar amfani da tsarin na’rorin fasaha, waɗanda za su tabbatar da cewa an yi bi sahihiyar hanyar tantance masu rajistar shaidar masu jefa ƙuri’a. Daga nan kuma za a loda sakamakon kai-tsaye daga rumfukan zaɓe zuwa shafukan rariyar tattara bayanan INEC, yadda kowa zai iya shiga ya duba sakamakon zaɓe tun a ranar da aka kaɗa ƙuri’a.

“Saboda haka dalili kenan aka ƙirƙiro BVAS da IReV. Kuma ba za mu fasa yin amfani da waɗannan tsare-tsare guda biyu ba a zaɓen 2023,” inji Yakubu.

Shugaban na INEC ya ce nan da makonni kaɗan hukumar sa za ta fara yin taron ganawa da manema labarai duk bayan sati biyu, domin ta riƙa sanar wa ‘yan Najeriya irin shirin da ta ke ciki dangane da tunkarar zaɓen 2023.

Ya ce idan zaɓen ya kusa ne INEC za ta riƙa yin taron zantawa da manema labarai a kowace rana.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gasar Kofin Kwallon Kafa 2022: Qatar Ta Haramta Hadadar Barasa A Filayen Wasanninta

Next Post

Kotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Zargin Damfarar N544m

Related

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

3 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

4 hours ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

6 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

7 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

15 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

16 hours ago
Next Post
Kotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Zargin Damfarar N544m

Kotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Zargin Damfarar N544m

LABARAI MASU NASABA

Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.