ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Da BVAS Da IReV Za Mu Yi Amfani Wajen Tattara Sakamakon Zabe – INEC

by Sulaiman
4 years ago
BVAS

Daidai ya rage saura kwanaki 100 a yi zaɓen shugaban ƙasa, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta jaddada cewa ba za ta taɓa fasa bin sabon tsarin ta na tattara sakamakon zaɓe da tantance yawan ƙuri’u na BVAS da IReV ba, domin tabbatar da sahihin zaɓe.

Shugaban INEC Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka, cikin wata sanarwar da hukumar ta fitar a ranar Laraba, inda ya ce an bijiro da tsarin amfani da BVAS da IReV ne domin hana murɗiya, maguɗi da satar akwati lokacin gudanar da zaɓen 2023.

  • 2023: INEC Ta Nemi Masu Kada Kuri’a Da Su Duba Sunayensu Cikin Wadanda Ta Yi Wa Rajista

Yakubu ya yi wannan ƙarin haske ranar Laraba, cikin jawabin da ya fitar daidai saura kwanaki 100 cif kafin a yi zaɓen shugaban ƙasa da na Majalisar Tarayya, wanda za a yi ranar 25 Ga Fabrairu 2023.

ADVERTISEMENT

Za a gudanar da zaɓen gwamnoni da na Majalisar Dokoki a ranar 11 Ga Maris, makonni biyu bayan zaɓen gwamna.

Kwanan nan wasu masu katsalandan sun yi ƙoƙarin kiran INEC da ta janye shirin yin amfani da na’urorin BVAS da IReV wajen tantance masu jefa ƙuri’a a lokacin da za a kaɗa ƙuri’u a zaɓen 2023.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Masu neman kada a yi amfani da BVAS da IReV sun ce gara a koma yin amfani da fallen takarda, wato fam wanda za a riƙa rubuta adadin ƙuri’un da kowane ɗan takara ko jam’iyya ta samu.

INEC ta daina amfani da wancan tsohon tsarin rubuta sakamako a fallayen takardu tun bayan ƙirƙiro tsarin BVAS da IReV, wanda ta ce da shi za ta yi amfani a zaɓen 2023.

A kan haka ne Yakubu ya ce tuni an shirya yin amfani da sabon tsarin a zaɓe mai zuwa, kuma ba za a fasa yin amfani da tsarin ba.

“Kamar yadda na sha nanatawa, INEC Nijeriya ta ke yi wa aiki, ba wata jam’iyya ko wani ɗan siyasa ba. ‘Yan Nijeriya mu ke wa aiki tare sadaukarwa. Saboda jama’a buƙatar sahihin zaɓe mai inganci, wanda zai zama karɓaɓɓe ta hanyar amfani da tsarin na’rorin fasaha, waɗanda za su tabbatar da cewa an yi bi sahihiyar hanyar tantance masu rajistar shaidar masu jefa ƙuri’a. Daga nan kuma za a loda sakamakon kai-tsaye daga rumfukan zaɓe zuwa shafukan rariyar tattara bayanan INEC, yadda kowa zai iya shiga ya duba sakamakon zaɓe tun a ranar da aka kaɗa ƙuri’a.

“Saboda haka dalili kenan aka ƙirƙiro BVAS da IReV. Kuma ba za mu fasa yin amfani da waɗannan tsare-tsare guda biyu ba a zaɓen 2023,” inji Yakubu.

Shugaban na INEC ya ce nan da makonni kaɗan hukumar sa za ta fara yin taron ganawa da manema labarai duk bayan sati biyu, domin ta riƙa sanar wa ‘yan Najeriya irin shirin da ta ke ciki dangane da tunkarar zaɓen 2023.

Ya ce idan zaɓen ya kusa ne INEC za ta riƙa yin taron zantawa da manema labarai a kowace rana.

BVAS
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Kotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Zargin Damfarar N544m

Kotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Zargin Damfarar N544m

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.