ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Da BVAS Da IReV Za Mu Yi Amfani Wajen Tattara Sakamakon Zabe – INEC

by Sulaiman
4 years ago
BVAS

Daidai ya rage saura kwanaki 100 a yi zaɓen shugaban ƙasa, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta jaddada cewa ba za ta taɓa fasa bin sabon tsarin ta na tattara sakamakon zaɓe da tantance yawan ƙuri’u na BVAS da IReV ba, domin tabbatar da sahihin zaɓe.

Shugaban INEC Mahmood Yakubu ne ya bayyana haka, cikin wata sanarwar da hukumar ta fitar a ranar Laraba, inda ya ce an bijiro da tsarin amfani da BVAS da IReV ne domin hana murɗiya, maguɗi da satar akwati lokacin gudanar da zaɓen 2023.

  • 2023: INEC Ta Nemi Masu Kada Kuri’a Da Su Duba Sunayensu Cikin Wadanda Ta Yi Wa Rajista

Yakubu ya yi wannan ƙarin haske ranar Laraba, cikin jawabin da ya fitar daidai saura kwanaki 100 cif kafin a yi zaɓen shugaban ƙasa da na Majalisar Tarayya, wanda za a yi ranar 25 Ga Fabrairu 2023.

ADVERTISEMENT

Za a gudanar da zaɓen gwamnoni da na Majalisar Dokoki a ranar 11 Ga Maris, makonni biyu bayan zaɓen gwamna.

Kwanan nan wasu masu katsalandan sun yi ƙoƙarin kiran INEC da ta janye shirin yin amfani da na’urorin BVAS da IReV wajen tantance masu jefa ƙuri’a a lokacin da za a kaɗa ƙuri’u a zaɓen 2023.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Masu neman kada a yi amfani da BVAS da IReV sun ce gara a koma yin amfani da fallen takarda, wato fam wanda za a riƙa rubuta adadin ƙuri’un da kowane ɗan takara ko jam’iyya ta samu.

INEC ta daina amfani da wancan tsohon tsarin rubuta sakamako a fallayen takardu tun bayan ƙirƙiro tsarin BVAS da IReV, wanda ta ce da shi za ta yi amfani a zaɓen 2023.

A kan haka ne Yakubu ya ce tuni an shirya yin amfani da sabon tsarin a zaɓe mai zuwa, kuma ba za a fasa yin amfani da tsarin ba.

“Kamar yadda na sha nanatawa, INEC Nijeriya ta ke yi wa aiki, ba wata jam’iyya ko wani ɗan siyasa ba. ‘Yan Nijeriya mu ke wa aiki tare sadaukarwa. Saboda jama’a buƙatar sahihin zaɓe mai inganci, wanda zai zama karɓaɓɓe ta hanyar amfani da tsarin na’rorin fasaha, waɗanda za su tabbatar da cewa an yi bi sahihiyar hanyar tantance masu rajistar shaidar masu jefa ƙuri’a. Daga nan kuma za a loda sakamakon kai-tsaye daga rumfukan zaɓe zuwa shafukan rariyar tattara bayanan INEC, yadda kowa zai iya shiga ya duba sakamakon zaɓe tun a ranar da aka kaɗa ƙuri’a.

“Saboda haka dalili kenan aka ƙirƙiro BVAS da IReV. Kuma ba za mu fasa yin amfani da waɗannan tsare-tsare guda biyu ba a zaɓen 2023,” inji Yakubu.

Shugaban na INEC ya ce nan da makonni kaɗan hukumar sa za ta fara yin taron ganawa da manema labarai duk bayan sati biyu, domin ta riƙa sanar wa ‘yan Najeriya irin shirin da ta ke ciki dangane da tunkarar zaɓen 2023.

Ya ce idan zaɓen ya kusa ne INEC za ta riƙa yin taron zantawa da manema labarai a kowace rana.

BVAS
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Kotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Zargin Damfarar N544m

Kotu Ta Wanke Babachir Lawal Daga Zargin Damfarar N544m

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.