• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gwamnan Bauchi Ya Ayyana Jatau A Matsayin Abokin Takararsa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Gwamnan Bauchi Ya Ayyana Jatau A Matsayin Abokin Takararsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Bauchi kuma dan takarar kujerar gwamnan Jihar na jam’iyyar PDP, Sanata Bala Muhammad, ya ayyana mambar Majalisar wakilai ta tarayya da ke wakiltar mazabar Zaki, Honorable Muhammad Auwal Jatau a matsayin abokin takararsa a zaben 2023 da ke tafe.

Honorable Jatau shi ne ya shelanta hakan a hirarsa da ‘yan jarida a Bauchi ranar Lahadi.

  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Nada Sabbin Kwamishinoni 6

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa Sanata Baba Tela shine mataimakin gwamnan Jihar a halin yanzu amma ba zai samu damar yin takara tare da gwamna Bala Muhammad ba a zaben 2023 sakamakon jingine shi a gefe da gwamnan ya yi.

Sabon abokin takarar ya gode wa gwamnan bisa zabinsa da ya yi a matsayin abokin da za su yi takara, sai ya sha alwashin yin kokari domin tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a jihar.

A cewarsa Muhammad Auwal Jatau, “Zan yi amfani da wannan damar wajen mika godiya ta musamman ga Allah (subhanahu wataala) da kasancewa ta a halin da na samu kaina a yau mataimakin dan takarar gwamnan Jihar, zan kuma mika godiya ta musamman wa shi gwamnanmu Bala Abdulkadir Mohammed da ya ga cewa ni na cancanta na zama mataimakinsa na cancanci na zama wanda zan yi aiki a karkashinsa ya ce ni din nan ya aminta ya yi aiki da ni.”

Labarai Masu Nasaba

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

“Babu wani abun da dan adam zai maka a duniya fiye da mutum ya ce ka zo ka kasance mai rike masa nan ka tallafa masa a lokacin da yake aiwatar da hidima irin ta jama’a, ta Gwamnati da ta mulki. Wannan abin godiya ne kuma ina cike da godiyan.

“Bahaushe ya ce zo mu ci tuwo ya fi tuwon dadi. Saboda haka ina mika godiya bisa amincewa da ni da ya yi bisa yarda a ya dauka ya daura min.”

Ya tabbatar da cewa wannan zabin da aka masa zai yi iyaka bakin kokarinsa wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a zaben 2023 tare da nasarar su, ya kuma ce zai yi biyayya wa gwamnan kuma zai kasance mai hakuri a kowani lokaci domin cimma nasarorin da aka sanya a gaba.

Da ya juya kan ayyukan gwamna Bala kuwa, ya misalta Gwamnatin Bala Muhammad a matsayin wacce ya shimfida ayyukan raya jihar fiye da kowace gwamnati da aka taba yi a jihar. Ya kuma tabbatar wa al’ummar jihar cewa zango na biyu na mulkin Bala Muhammad za ta zarce na farko ta fuskacin shimfida ayyukan raya jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwa: Mutum 4 Sun Mutu, 8,400 Sun Bar Gidajensu A Adamawa

Next Post

Rasuwar Sarkin Funakaye, An Yi Babban Rashi – Gwamna Inuwa

Related

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

3 hours ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

1 day ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

4 days ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

5 days ago
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa
Siyasa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

1 week ago
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC
Siyasa

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

1 week ago
Next Post
Rasuwar Sarkin Funakaye, An Yi Babban Rashi – Gwamna Inuwa

Rasuwar Sarkin Funakaye, An Yi Babban Rashi - Gwamna Inuwa

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.