• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gwamnan Bauchi Ya Ayyana Jatau A Matsayin Abokin Takararsa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Gwamnan Bauchi Ya Ayyana Jatau A Matsayin Abokin Takararsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Bauchi kuma dan takarar kujerar gwamnan Jihar na jam’iyyar PDP, Sanata Bala Muhammad, ya ayyana mambar Majalisar wakilai ta tarayya da ke wakiltar mazabar Zaki, Honorable Muhammad Auwal Jatau a matsayin abokin takararsa a zaben 2023 da ke tafe.

Honorable Jatau shi ne ya shelanta hakan a hirarsa da ‘yan jarida a Bauchi ranar Lahadi.

  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Nada Sabbin Kwamishinoni 6

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa Sanata Baba Tela shine mataimakin gwamnan Jihar a halin yanzu amma ba zai samu damar yin takara tare da gwamna Bala Muhammad ba a zaben 2023 sakamakon jingine shi a gefe da gwamnan ya yi.

Sabon abokin takarar ya gode wa gwamnan bisa zabinsa da ya yi a matsayin abokin da za su yi takara, sai ya sha alwashin yin kokari domin tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a jihar.

A cewarsa Muhammad Auwal Jatau, “Zan yi amfani da wannan damar wajen mika godiya ta musamman ga Allah (subhanahu wataala) da kasancewa ta a halin da na samu kaina a yau mataimakin dan takarar gwamnan Jihar, zan kuma mika godiya ta musamman wa shi gwamnanmu Bala Abdulkadir Mohammed da ya ga cewa ni na cancanta na zama mataimakinsa na cancanci na zama wanda zan yi aiki a karkashinsa ya ce ni din nan ya aminta ya yi aiki da ni.”

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

“Babu wani abun da dan adam zai maka a duniya fiye da mutum ya ce ka zo ka kasance mai rike masa nan ka tallafa masa a lokacin da yake aiwatar da hidima irin ta jama’a, ta Gwamnati da ta mulki. Wannan abin godiya ne kuma ina cike da godiyan.

“Bahaushe ya ce zo mu ci tuwo ya fi tuwon dadi. Saboda haka ina mika godiya bisa amincewa da ni da ya yi bisa yarda a ya dauka ya daura min.”

Ya tabbatar da cewa wannan zabin da aka masa zai yi iyaka bakin kokarinsa wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a zaben 2023 tare da nasarar su, ya kuma ce zai yi biyayya wa gwamnan kuma zai kasance mai hakuri a kowani lokaci domin cimma nasarorin da aka sanya a gaba.

Da ya juya kan ayyukan gwamna Bala kuwa, ya misalta Gwamnatin Bala Muhammad a matsayin wacce ya shimfida ayyukan raya jihar fiye da kowace gwamnati da aka taba yi a jihar. Ya kuma tabbatar wa al’ummar jihar cewa zango na biyu na mulkin Bala Muhammad za ta zarce na farko ta fuskacin shimfida ayyukan raya jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ambaliyar Ruwa: Mutum 4 Sun Mutu, 8,400 Sun Bar Gidajensu A Adamawa

Next Post

Rasuwar Sarkin Funakaye, An Yi Babban Rashi – Gwamna Inuwa

Related

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

16 hours ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

1 day ago
Gwamnan Abba Kabir Yusuf tare da Arch. Ali Hassan
Tattaunawa

Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan

2 days ago
2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega
Siyasa

2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega

2 days ago
Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano
Siyasa

Ƴansanda Sun Gargaɗi Masu Lalata Fastar Tinubu A Kano

4 days ago
Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista
Manyan Labarai

Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

4 days ago
Next Post
Rasuwar Sarkin Funakaye, An Yi Babban Rashi – Gwamna Inuwa

Rasuwar Sarkin Funakaye, An Yi Babban Rashi - Gwamna Inuwa

LABARAI MASU NASABA

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.