• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gwamnan Bauchi Ya Ayyana Jatau A Matsayin Abokin Takararsa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi kuma dan takarar kujerar gwamnan Jihar na jam’iyyar PDP, Sanata Bala Muhammad, ya ayyana mambar Majalisar wakilai ta tarayya da ke wakiltar mazabar Zaki, Honorable Muhammad Auwal Jatau a matsayin abokin takararsa a zaben 2023 da ke tafe.

Honorable Jatau shi ne ya shelanta hakan a hirarsa da ‘yan jarida a Bauchi ranar Lahadi.

  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Nada Sabbin Kwamishinoni 6

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa Sanata Baba Tela shine mataimakin gwamnan Jihar a halin yanzu amma ba zai samu damar yin takara tare da gwamna Bala Muhammad ba a zaben 2023 sakamakon jingine shi a gefe da gwamnan ya yi.

Sabon abokin takarar ya gode wa gwamnan bisa zabinsa da ya yi a matsayin abokin da za su yi takara, sai ya sha alwashin yin kokari domin tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a jihar.

A cewarsa Muhammad Auwal Jatau, “Zan yi amfani da wannan damar wajen mika godiya ta musamman ga Allah (subhanahu wataala) da kasancewa ta a halin da na samu kaina a yau mataimakin dan takarar gwamnan Jihar, zan kuma mika godiya ta musamman wa shi gwamnanmu Bala Abdulkadir Mohammed da ya ga cewa ni na cancanta na zama mataimakinsa na cancanci na zama wanda zan yi aiki a karkashinsa ya ce ni din nan ya aminta ya yi aiki da ni.”

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

“Babu wani abun da dan adam zai maka a duniya fiye da mutum ya ce ka zo ka kasance mai rike masa nan ka tallafa masa a lokacin da yake aiwatar da hidima irin ta jama’a, ta Gwamnati da ta mulki. Wannan abin godiya ne kuma ina cike da godiyan.

“Bahaushe ya ce zo mu ci tuwo ya fi tuwon dadi. Saboda haka ina mika godiya bisa amincewa da ni da ya yi bisa yarda a ya dauka ya daura min.”

Ya tabbatar da cewa wannan zabin da aka masa zai yi iyaka bakin kokarinsa wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a zaben 2023 tare da nasarar su, ya kuma ce zai yi biyayya wa gwamnan kuma zai kasance mai hakuri a kowani lokaci domin cimma nasarorin da aka sanya a gaba.

Da ya juya kan ayyukan gwamna Bala kuwa, ya misalta Gwamnatin Bala Muhammad a matsayin wacce ya shimfida ayyukan raya jihar fiye da kowace gwamnati da aka taba yi a jihar. Ya kuma tabbatar wa al’ummar jihar cewa zango na biyu na mulkin Bala Muhammad za ta zarce na farko ta fuskacin shimfida ayyukan raya jihar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP
Siyasa

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan
Manyan Labarai

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Next Post
Rasuwar Sarkin Funakaye, An Yi Babban Rashi – Gwamna Inuwa

Rasuwar Sarkin Funakaye, An Yi Babban Rashi - Gwamna Inuwa

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025
Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 

October 14, 2025
Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

Sin Tana Adawa Da Matakan Kuntatawa Na Amurka Kan Bangarorin Kasar Da Suka Shafi Harkokin Teku Da Jigila Da Ginin Jiragen Ruwa 

October 14, 2025
Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.