ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Gwamnan Bauchi Ya Ayyana Jatau A Matsayin Abokin Takararsa

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Bauchi

Gwamnan Jihar Bauchi kuma dan takarar kujerar gwamnan Jihar na jam’iyyar PDP, Sanata Bala Muhammad, ya ayyana mambar Majalisar wakilai ta tarayya da ke wakiltar mazabar Zaki, Honorable Muhammad Auwal Jatau a matsayin abokin takararsa a zaben 2023 da ke tafe.

Honorable Jatau shi ne ya shelanta hakan a hirarsa da ‘yan jarida a Bauchi ranar Lahadi.

  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Nada Sabbin Kwamishinoni 6

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewa Sanata Baba Tela shine mataimakin gwamnan Jihar a halin yanzu amma ba zai samu damar yin takara tare da gwamna Bala Muhammad ba a zaben 2023 sakamakon jingine shi a gefe da gwamnan ya yi.

ADVERTISEMENT

Sabon abokin takarar ya gode wa gwamnan bisa zabinsa da ya yi a matsayin abokin da za su yi takara, sai ya sha alwashin yin kokari domin tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a jihar.

A cewarsa Muhammad Auwal Jatau, “Zan yi amfani da wannan damar wajen mika godiya ta musamman ga Allah (subhanahu wataala) da kasancewa ta a halin da na samu kaina a yau mataimakin dan takarar gwamnan Jihar, zan kuma mika godiya ta musamman wa shi gwamnanmu Bala Abdulkadir Mohammed da ya ga cewa ni na cancanta na zama mataimakinsa na cancanci na zama wanda zan yi aiki a karkashinsa ya ce ni din nan ya aminta ya yi aiki da ni.”

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

“Babu wani abun da dan adam zai maka a duniya fiye da mutum ya ce ka zo ka kasance mai rike masa nan ka tallafa masa a lokacin da yake aiwatar da hidima irin ta jama’a, ta Gwamnati da ta mulki. Wannan abin godiya ne kuma ina cike da godiyan.

“Bahaushe ya ce zo mu ci tuwo ya fi tuwon dadi. Saboda haka ina mika godiya bisa amincewa da ni da ya yi bisa yarda a ya dauka ya daura min.”

Ya tabbatar da cewa wannan zabin da aka masa zai yi iyaka bakin kokarinsa wajen tabbatar da nasarar jam’iyyar PDP a zaben 2023 tare da nasarar su, ya kuma ce zai yi biyayya wa gwamnan kuma zai kasance mai hakuri a kowani lokaci domin cimma nasarorin da aka sanya a gaba.

Da ya juya kan ayyukan gwamna Bala kuwa, ya misalta Gwamnatin Bala Muhammad a matsayin wacce ya shimfida ayyukan raya jihar fiye da kowace gwamnati da aka taba yi a jihar. Ya kuma tabbatar wa al’ummar jihar cewa zango na biyu na mulkin Bala Muhammad za ta zarce na farko ta fuskacin shimfida ayyukan raya jihar.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Rasuwar Sarkin Funakaye, An Yi Babban Rashi – Gwamna Inuwa

Rasuwar Sarkin Funakaye, An Yi Babban Rashi - Gwamna Inuwa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.