ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: INEC Ta Tsame Sunayen Wadanda Suka Yi Rajista Sau Biyu

by Sulaiman
3 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce za ta fara raba Katin Zaɓe na Dindindin (PVC) a cikin Oktoba da kuma Nuwamba, tare da kakka:ɓe sunayen duk waɗanda suka yi rajista sau biyu ko fiye da haka.

Kwamishinan INEC na Ƙasa kuma Jami’in Yaɗa Labarai na Hukumar Zaɓe, Mista Festus Okoye, shi ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke lura da aikin rajistar katin zaɓe a ranar Asabar a Auka, Jihar Anambra.

  • Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 

Okoye, wanda shi ne mai lura da aikin rajistar katin zaɓe a jihohin Abiya, Anambra da Binuwai, ya ce INEC ta na aikin rajistar ne a tsanake, “ta yadda za a kakkaɓe sunayen waɗanda su ka yi rajista sau biyu ko fiye da sau biyu kafin a buga katin shaidar rajistar zaɓe har a rarraba su cikin Oktoba da Nuwamba.”

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Dokar zaɓe kuma ta umarci INEC ta kafa sunayen waɗanda aka yi wa rajista a dukkan ƙananan hukumomi 774 da kuma Cibiyoyin Rajista 8,809 da ake da su a ƙasar nan, domin jama’a su tantance sunayen su kuma masu ƙorafe-ƙorafe su yi.

“Sannan kuma za a buga Katin Zaɓe na Dindindin (PVC), a loda su a motoci zuwa kowace ƙaramar hukuma.”

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

Okoye ya ja hankalin jama’a cewa ɓata lokaci ne a ce mutum ya je ya yi rajista, amma ya kasa karɓar katin zaɓen sa. “Saboda tilas sai da katin zaɓe ne kaɗai mutum zai iya jefa ƙuri’a.”

Ya ce waɗanda aka yi wa rajista tsakanin Janairu zuwa Yuni za su karɓi katin zaɓen su cikin Oktoba. Su kuma waɗanda aka yi wa rajista daga 1 zuwa 31 ga Yuli, za su karɓi nasu katin zaɓen cikin Nuwamba.

Hukumar Zaɓe ta bijiro da sabunta rajistar katin zaɓe ne saboda dalilai da dama, waɗanda su ka haɗa da: samun damar yin rajista ga duk wani ɗan Nijeriya da ya kai shekara 18 daga 2019 zuwa 2022. Saboda ta hanyar mallakar rajista ne kaɗai wanda ya cika shekara 18 bayan 2018 zai iya yin zaɓe.

Haka kuma wanda bai samu damar yin rajista ta katin zaɓe a 2018 ba, ya samu damar yi a wannan lokacin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026
Labarai

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
Labarai

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Next Post
Bayan Shafe Shekaru Yana Adawa Da Buhari, Orubebe Ya Koma APC

Bayan Shafe Shekaru Yana Adawa Da Buhari, Orubebe Ya Koma APC

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.