• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: INEC Ta Tsame Sunayen Wadanda Suka Yi Rajista Sau Biyu

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
2023: INEC Ta Tsame Sunayen Wadanda Suka Yi Rajista Sau Biyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce za ta fara raba Katin Zaɓe na Dindindin (PVC) a cikin Oktoba da kuma Nuwamba, tare da kakka:ɓe sunayen duk waɗanda suka yi rajista sau biyu ko fiye da haka.

Kwamishinan INEC na Ƙasa kuma Jami’in Yaɗa Labarai na Hukumar Zaɓe, Mista Festus Okoye, shi ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke lura da aikin rajistar katin zaɓe a ranar Asabar a Auka, Jihar Anambra.

  • Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 

Okoye, wanda shi ne mai lura da aikin rajistar katin zaɓe a jihohin Abiya, Anambra da Binuwai, ya ce INEC ta na aikin rajistar ne a tsanake, “ta yadda za a kakkaɓe sunayen waɗanda su ka yi rajista sau biyu ko fiye da sau biyu kafin a buga katin shaidar rajistar zaɓe har a rarraba su cikin Oktoba da Nuwamba.”

Ya ce, “Dokar zaɓe kuma ta umarci INEC ta kafa sunayen waɗanda aka yi wa rajista a dukkan ƙananan hukumomi 774 da kuma Cibiyoyin Rajista 8,809 da ake da su a ƙasar nan, domin jama’a su tantance sunayen su kuma masu ƙorafe-ƙorafe su yi.

“Sannan kuma za a buga Katin Zaɓe na Dindindin (PVC), a loda su a motoci zuwa kowace ƙaramar hukuma.”

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Okoye ya ja hankalin jama’a cewa ɓata lokaci ne a ce mutum ya je ya yi rajista, amma ya kasa karɓar katin zaɓen sa. “Saboda tilas sai da katin zaɓe ne kaɗai mutum zai iya jefa ƙuri’a.”

Ya ce waɗanda aka yi wa rajista tsakanin Janairu zuwa Yuni za su karɓi katin zaɓen su cikin Oktoba. Su kuma waɗanda aka yi wa rajista daga 1 zuwa 31 ga Yuli, za su karɓi nasu katin zaɓen cikin Nuwamba.

Hukumar Zaɓe ta bijiro da sabunta rajistar katin zaɓe ne saboda dalilai da dama, waɗanda su ka haɗa da: samun damar yin rajista ga duk wani ɗan Nijeriya da ya kai shekara 18 daga 2019 zuwa 2022. Saboda ta hanyar mallakar rajista ne kaɗai wanda ya cika shekara 18 bayan 2018 zai iya yin zaɓe.

Haka kuma wanda bai samu damar yin rajista ta katin zaɓe a 2018 ba, ya samu damar yi a wannan lokacin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Malaman KASU Sun Janye Yajin Aiki Bayan Barazanar El-Rufa’i 

Next Post

Bayan Shafe Shekaru Yana Adawa Da Buhari, Orubebe Ya Koma APC

Related

Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

2 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

3 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

3 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

5 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

7 hours ago
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai
Labarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

7 hours ago
Next Post
Bayan Shafe Shekaru Yana Adawa Da Buhari, Orubebe Ya Koma APC

Bayan Shafe Shekaru Yana Adawa Da Buhari, Orubebe Ya Koma APC

LABARAI MASU NASABA

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.