ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: INEC Ta Tsame Sunayen Wadanda Suka Yi Rajista Sau Biyu

by Sulaiman
4 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce za ta fara raba Katin Zaɓe na Dindindin (PVC) a cikin Oktoba da kuma Nuwamba, tare da kakka:ɓe sunayen duk waɗanda suka yi rajista sau biyu ko fiye da haka.

Kwamishinan INEC na Ƙasa kuma Jami’in Yaɗa Labarai na Hukumar Zaɓe, Mista Festus Okoye, shi ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke lura da aikin rajistar katin zaɓe a ranar Asabar a Auka, Jihar Anambra.

  • Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 

Okoye, wanda shi ne mai lura da aikin rajistar katin zaɓe a jihohin Abiya, Anambra da Binuwai, ya ce INEC ta na aikin rajistar ne a tsanake, “ta yadda za a kakkaɓe sunayen waɗanda su ka yi rajista sau biyu ko fiye da sau biyu kafin a buga katin shaidar rajistar zaɓe har a rarraba su cikin Oktoba da Nuwamba.”

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Dokar zaɓe kuma ta umarci INEC ta kafa sunayen waɗanda aka yi wa rajista a dukkan ƙananan hukumomi 774 da kuma Cibiyoyin Rajista 8,809 da ake da su a ƙasar nan, domin jama’a su tantance sunayen su kuma masu ƙorafe-ƙorafe su yi.

“Sannan kuma za a buga Katin Zaɓe na Dindindin (PVC), a loda su a motoci zuwa kowace ƙaramar hukuma.”

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Okoye ya ja hankalin jama’a cewa ɓata lokaci ne a ce mutum ya je ya yi rajista, amma ya kasa karɓar katin zaɓen sa. “Saboda tilas sai da katin zaɓe ne kaɗai mutum zai iya jefa ƙuri’a.”

Ya ce waɗanda aka yi wa rajista tsakanin Janairu zuwa Yuni za su karɓi katin zaɓen su cikin Oktoba. Su kuma waɗanda aka yi wa rajista daga 1 zuwa 31 ga Yuli, za su karɓi nasu katin zaɓen cikin Nuwamba.

Hukumar Zaɓe ta bijiro da sabunta rajistar katin zaɓe ne saboda dalilai da dama, waɗanda su ka haɗa da: samun damar yin rajista ga duk wani ɗan Nijeriya da ya kai shekara 18 daga 2019 zuwa 2022. Saboda ta hanyar mallakar rajista ne kaɗai wanda ya cika shekara 18 bayan 2018 zai iya yin zaɓe.

Haka kuma wanda bai samu damar yin rajista ta katin zaɓe a 2018 ba, ya samu damar yi a wannan lokacin.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Bayan Shafe Shekaru Yana Adawa Da Buhari, Orubebe Ya Koma APC

Bayan Shafe Shekaru Yana Adawa Da Buhari, Orubebe Ya Koma APC

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.