ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: INEC Ta Tsame Sunayen Wadanda Suka Yi Rajista Sau Biyu

by Sulaiman
4 years ago
INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ce za ta fara raba Katin Zaɓe na Dindindin (PVC) a cikin Oktoba da kuma Nuwamba, tare da kakka:ɓe sunayen duk waɗanda suka yi rajista sau biyu ko fiye da haka.

Kwamishinan INEC na Ƙasa kuma Jami’in Yaɗa Labarai na Hukumar Zaɓe, Mista Festus Okoye, shi ne ya bayyana haka a lokacin da ya ke lura da aikin rajistar katin zaɓe a ranar Asabar a Auka, Jihar Anambra.

  • Wayar Da Kai: INEC Za Ta Hada Hannu Da Kungiyar ‘Darika Awareness Forum Katsina’ 

Okoye, wanda shi ne mai lura da aikin rajistar katin zaɓe a jihohin Abiya, Anambra da Binuwai, ya ce INEC ta na aikin rajistar ne a tsanake, “ta yadda za a kakkaɓe sunayen waɗanda su ka yi rajista sau biyu ko fiye da sau biyu kafin a buga katin shaidar rajistar zaɓe har a rarraba su cikin Oktoba da Nuwamba.”

ADVERTISEMENT

Ya ce, “Dokar zaɓe kuma ta umarci INEC ta kafa sunayen waɗanda aka yi wa rajista a dukkan ƙananan hukumomi 774 da kuma Cibiyoyin Rajista 8,809 da ake da su a ƙasar nan, domin jama’a su tantance sunayen su kuma masu ƙorafe-ƙorafe su yi.

“Sannan kuma za a buga Katin Zaɓe na Dindindin (PVC), a loda su a motoci zuwa kowace ƙaramar hukuma.”

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Okoye ya ja hankalin jama’a cewa ɓata lokaci ne a ce mutum ya je ya yi rajista, amma ya kasa karɓar katin zaɓen sa. “Saboda tilas sai da katin zaɓe ne kaɗai mutum zai iya jefa ƙuri’a.”

Ya ce waɗanda aka yi wa rajista tsakanin Janairu zuwa Yuni za su karɓi katin zaɓen su cikin Oktoba. Su kuma waɗanda aka yi wa rajista daga 1 zuwa 31 ga Yuli, za su karɓi nasu katin zaɓen cikin Nuwamba.

Hukumar Zaɓe ta bijiro da sabunta rajistar katin zaɓe ne saboda dalilai da dama, waɗanda su ka haɗa da: samun damar yin rajista ga duk wani ɗan Nijeriya da ya kai shekara 18 daga 2019 zuwa 2022. Saboda ta hanyar mallakar rajista ne kaɗai wanda ya cika shekara 18 bayan 2018 zai iya yin zaɓe.

Haka kuma wanda bai samu damar yin rajista ta katin zaɓe a 2018 ba, ya samu damar yi a wannan lokacin.

INEC
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

MASU ALAKA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Next Post
Bayan Shafe Shekaru Yana Adawa Da Buhari, Orubebe Ya Koma APC

Bayan Shafe Shekaru Yana Adawa Da Buhari, Orubebe Ya Koma APC

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.