• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Manyan Jiragen Ruwa 75,000 Suka Yi Hada-hada A Tashar Lekki

by Bello Hamza
1 year ago
in Tattalin Arziki
0
lekki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata ne hukumar kula da tashar jiragen ruwa na ‘Lekki Deep Seaport’ ta bayyana cewa, ta samu nasarar mu’amala da manyan jiragen ruwa 75,000, ta karbi wasu kananan jirage 25,000 haka kuma kwantaina 100,000 aka sauke a cikin shekarar data gabata.

Sanarwa haka ta fito ne daga bayanin da hukumar tashar ta yi a shafinta na D don murnar cika shekara 1 da fara harkokin kasuwanci a tashar, inda aka fara a ranar 1 gaa watan Afrilu 2023. An yi haka ne don kuma a duba yadda aka gudanar da aikin tashar a cikin shekara da ta gabata. Sanarwar ta ce, a cikin shekarar ne tashar ta karbi babban jirgi dauke da iskar gas ‘LNG-powered bessel’ mai nauyin 366 LOA.

  • FCTA Ta Rushe Gidaje Dubu 15 Da Aka Gina Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Unguwar Gwarinpa Da Ke Abuja
  • Kotu Ta Tsare Wani Mutum Kan Yi Wa ‘Yar Shekaru 11 Ciki A Legas

Haka kuma a 2023 tashar ta samu nasarar gudanar da harkokin karbar kayayyaki da aka fi sani da “Transshipment” har guda 25,000 daga watan Yuni 2023 zuwa yanzu.

Bayani ya kuma nuna cewa, tashar ta samu nasarar karbar kwantaina 100,000 ba tare da wata mastala ba, wannan ke kara nuna cewa, tashar a shirye take na shiga tsarin kasuwanci a duniya.

Tashar ta kuma mika godiya bisa goyon bayan da take samu daga Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya (NPA), ta kuma nemi a ci gaba da samun irin wannan hadin kan.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

Daga nan sun mika godiya da jinjina ga dukkan masu ruwa da tsaki da suka hada da Ministan Tattalin Arzikin Teku, Adegboyega Oyetola, Shugaban NPA, Mohammed Bello-Koko, Shugaban Hukumar Kwastam, Adewale Adeniyi da shugababn hukumar NEPZA, Dr. Olufemi Ogunyemi, da sauran su.

“Muna kuma mika godiya ga shugabanninmu, kamar Mr Biodun Dabiri, Alhaji Bode Oyedele, Mr Haresh Aswani, Mr Mohammed Bello-Koko, Mr Nabin Nahata, Mr Wu Di, Mr Steben Liu da Mr Dinesh Rathi a bisa goyon bayan da suke ba mu har muka samu wannan nasarar”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Sa Ran Samun Tafiye-tafiyen Fasinjoji Fiye Da Miliyan 750 Yayin Hutun Bikin Qingming

Next Post

Bayar Da Tallafin Wutar Lantarki Kaso 85 na Kara Nuna Tinubu Mai Kishin Jama’a Ne – Minista

Related

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

7 days ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

4 weeks ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

4 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA

1 month ago
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Yi Amafani Da Damar Fitar Da Kaya Zuwa Ketare

1 month ago
Next Post
lekki

Bayar Da Tallafin Wutar Lantarki Kaso 85 na Kara Nuna Tinubu Mai Kishin Jama'a Ne - Minista

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

May 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

May 30, 2025
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

May 30, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 30-03-2025

May 30, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano

An Kama Mutane 49 Da Ake Zargi Da Damfara A Jihar Kogi

May 30, 2025
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (2)

May 30, 2025
Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

Duk Da Janye Tallafin Rarar Mai, Matsin Rayuwa Na Addabar ‘Yan Nijeriya

May 30, 2025
Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

May 30, 2025
Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

May 30, 2025
Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.