ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Danyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.436 —OPEC

by Abubakar Abba
6 months ago
OPEC

Danyen Mai da aka hako a kasar nan a watan Nuwambar shekarar 2025 ya dan karu zuwa Ganguna miliyan 1.436 a kullum.

Ya karu ne daga Ganguna miliyan 1.401 a cikin watan Okutobar shekarar 2025.

  • Yadda Kasar Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakan Kwastam Na Musamman A Dukkanin Fadin Yankin Cinikayya Cikin ’Yanci Na Hainan Ya Jawo Hankalin Duniya Sosai
  • Tinubu Zai Gabatar Da Daftarin Kasafin Kuɗin 2026 Ga Majalisun Tarayya

Wannan bayanin na kunshe ne a cikin rahoton wata – wata na kungiyar OPEC da ta fitar, a ranar Alhamis da ta gabata.

ADVERTISEMENT

Duk da wannan adadin danyen man da kasar ta hako, har yanzu, ta gaza samar da adadin da kungiyar ta OPEC ta ayyana, kasar ta samar wanda hakan ya kai, kusan a watanni hudu a jere.

Watan Yulin shekarar 2025 lokaci na karshe da Nijeriya ta iya cimma afadin Gangunan danyen man da ake bukata.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Bisa wasu alkaluma da kungiyar ta OPEC ta fitar sun nuna cewa, a zango na uku na shekarar 2025_ Nijeriya ta hako Gangunan danyen mai miliyan 1.444 wanda kuma ya yi kasa da Gangunan danyen mai miliyan 1.481 da aka hako a kasar a zango na biyu da kuma wanda aka hako a zango na daya, da ya kai Ganguna miliyan 1.468.

Wannan lamarin, na yin nuni ne, da kokarin da ake ci gaba da yi, na ganin an daidaita yadda ake hako danyen man a kasar nan tare da kuma kokarin da Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da yi, na kara habaka fannin na hako danyen man a kasar.

Nan da shekara mai zuwa, kungiyar ta OPEC, da kuma sauran kasashen da ke hako danyen man, na son ganin suna hako adadinsa da ya kai na Ganguna miliyan 43, a kullum.

Kasashen na son cimma hakan ne, musamman domin su cike gibin bukatar da ake da shi.

Bugu da kari, duba da yadda nayin kasuwarsa ta kasance, manyan kasashen da ke hako danyen man a karkashin rukunin OPEC+ wadanda kuma kasar Saudiyya ke jagorantarsu, a watan da ya gabata sun amince za su dan dakatar da yawan adadin danyen man da suke hakowa, har zuwa dangon farko na shekarar 2026, musamman duba da cewa, sun hako danyen man da yawa a shekarar 2025.

Gazawar Nijeriya na hako yawan adadin danyen man, na ci gaba zama wata barazana gaga samarwa da kasar kudaden musaya na kasar waje musamman duba da cewa, fannin na hako danyen man, ya kasance daya daga cikin manyan hanyoyin samun kudaden shiga. Sai dai, wasu masana a fannin sun yi hasashen cewa, wannan ‘yar karuwar da aka samu ta hako danyen man, wata alama ce ta sake farfadowar fannin wanda kuma, dai kara karfafa samar da daidaito ga fannin.

Bugu da kari, kokarin da Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da yi, na gyaran matatun mai mallakar ta da kuma kokarin janyo hankalin masu duba hannun jari ga fannin kamar irinsu Dangote, hakan, zai kara bunkasa fannin a shekarar 2026.

Hakazalika, wasu kwararru a fannin, na ganin ya zama wajibi a dauki matakan gaggawa kan batun magance matsalolin rashin tsaro da dakile masu fasa Bututun mai da samar da ingantattun kayan aiki,matukar ana son a samar da ci gaba mai dorewa ga fannin.

OPEC
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoma 67 Suka Amfana Da Horon Cibiyar  NIHORT
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilan Da Suka Sa Fannin Kiwo Ke Fuskantar Kalubale A Nijeriya —Gwamnatin Tarayya

MASU ALAKA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN
Tattalin Arziki

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Next Post
Babu Wani Annabi Mai Daraja Kusa Da Ta Muhammad Rasulullah (SAW)

Babu Wani Annabi Mai Daraja Kusa Da Ta Muhammad Rasulullah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.