Danyen Mai da aka hako a kasar nan a watan Nuwambar shekarar 2025 ya dan karu zuwa Ganguna miliyan 1.436 a kullum.
Ya karu ne daga Ganguna miliyan 1.401 a cikin watan Okutobar shekarar 2025.
- Yadda Kasar Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakan Kwastam Na Musamman A Dukkanin Fadin Yankin Cinikayya Cikin ’Yanci Na Hainan Ya Jawo Hankalin Duniya Sosai
- Tinubu Zai Gabatar Da Daftarin Kasafin Kuɗin 2026 Ga Majalisun Tarayya
Wannan bayanin na kunshe ne a cikin rahoton wata – wata na kungiyar OPEC da ta fitar, a ranar Alhamis da ta gabata.
Duk da wannan adadin danyen man da kasar ta hako, har yanzu, ta gaza samar da adadin da kungiyar ta OPEC ta ayyana, kasar ta samar wanda hakan ya kai, kusan a watanni hudu a jere.
Watan Yulin shekarar 2025 lokaci na karshe da Nijeriya ta iya cimma afadin Gangunan danyen man da ake bukata.
Bisa wasu alkaluma da kungiyar ta OPEC ta fitar sun nuna cewa, a zango na uku na shekarar 2025_ Nijeriya ta hako Gangunan danyen mai miliyan 1.444 wanda kuma ya yi kasa da Gangunan danyen mai miliyan 1.481 da aka hako a kasar a zango na biyu da kuma wanda aka hako a zango na daya, da ya kai Ganguna miliyan 1.468.
Wannan lamarin, na yin nuni ne, da kokarin da ake ci gaba da yi, na ganin an daidaita yadda ake hako danyen man a kasar nan tare da kuma kokarin da Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da yi, na kara habaka fannin na hako danyen man a kasar.
Nan da shekara mai zuwa, kungiyar ta OPEC, da kuma sauran kasashen da ke hako danyen man, na son ganin suna hako adadinsa da ya kai na Ganguna miliyan 43, a kullum.
Kasashen na son cimma hakan ne, musamman domin su cike gibin bukatar da ake da shi.
Bugu da kari, duba da yadda nayin kasuwarsa ta kasance, manyan kasashen da ke hako danyen man a karkashin rukunin OPEC+ wadanda kuma kasar Saudiyya ke jagorantarsu, a watan da ya gabata sun amince za su dan dakatar da yawan adadin danyen man da suke hakowa, har zuwa dangon farko na shekarar 2026, musamman duba da cewa, sun hako danyen man da yawa a shekarar 2025.
Gazawar Nijeriya na hako yawan adadin danyen man, na ci gaba zama wata barazana gaga samarwa da kasar kudaden musaya na kasar waje musamman duba da cewa, fannin na hako danyen man, ya kasance daya daga cikin manyan hanyoyin samun kudaden shiga. Sai dai, wasu masana a fannin sun yi hasashen cewa, wannan ‘yar karuwar da aka samu ta hako danyen man, wata alama ce ta sake farfadowar fannin wanda kuma, dai kara karfafa samar da daidaito ga fannin.
Bugu da kari, kokarin da Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da yi, na gyaran matatun mai mallakar ta da kuma kokarin janyo hankalin masu duba hannun jari ga fannin kamar irinsu Dangote, hakan, zai kara bunkasa fannin a shekarar 2026.
Hakazalika, wasu kwararru a fannin, na ganin ya zama wajibi a dauki matakan gaggawa kan batun magance matsalolin rashin tsaro da dakile masu fasa Bututun mai da samar da ingantattun kayan aiki,matukar ana son a samar da ci gaba mai dorewa ga fannin.













