ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Danyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.436 —OPEC

by Abubakar Abba
7 months ago
OPEC

Danyen Mai da aka hako a kasar nan a watan Nuwambar shekarar 2025 ya dan karu zuwa Ganguna miliyan 1.436 a kullum.

Ya karu ne daga Ganguna miliyan 1.401 a cikin watan Okutobar shekarar 2025.

  • Yadda Kasar Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakan Kwastam Na Musamman A Dukkanin Fadin Yankin Cinikayya Cikin ’Yanci Na Hainan Ya Jawo Hankalin Duniya Sosai
  • Tinubu Zai Gabatar Da Daftarin Kasafin Kuɗin 2026 Ga Majalisun Tarayya

Wannan bayanin na kunshe ne a cikin rahoton wata – wata na kungiyar OPEC da ta fitar, a ranar Alhamis da ta gabata.

ADVERTISEMENT

Duk da wannan adadin danyen man da kasar ta hako, har yanzu, ta gaza samar da adadin da kungiyar ta OPEC ta ayyana, kasar ta samar wanda hakan ya kai, kusan a watanni hudu a jere.

Watan Yulin shekarar 2025 lokaci na karshe da Nijeriya ta iya cimma afadin Gangunan danyen man da ake bukata.

LABARAI MASU NASABA

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

Bisa wasu alkaluma da kungiyar ta OPEC ta fitar sun nuna cewa, a zango na uku na shekarar 2025_ Nijeriya ta hako Gangunan danyen mai miliyan 1.444 wanda kuma ya yi kasa da Gangunan danyen mai miliyan 1.481 da aka hako a kasar a zango na biyu da kuma wanda aka hako a zango na daya, da ya kai Ganguna miliyan 1.468.

Wannan lamarin, na yin nuni ne, da kokarin da ake ci gaba da yi, na ganin an daidaita yadda ake hako danyen man a kasar nan tare da kuma kokarin da Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da yi, na kara habaka fannin na hako danyen man a kasar.

Nan da shekara mai zuwa, kungiyar ta OPEC, da kuma sauran kasashen da ke hako danyen man, na son ganin suna hako adadinsa da ya kai na Ganguna miliyan 43, a kullum.

Kasashen na son cimma hakan ne, musamman domin su cike gibin bukatar da ake da shi.

Bugu da kari, duba da yadda nayin kasuwarsa ta kasance, manyan kasashen da ke hako danyen man a karkashin rukunin OPEC+ wadanda kuma kasar Saudiyya ke jagorantarsu, a watan da ya gabata sun amince za su dan dakatar da yawan adadin danyen man da suke hakowa, har zuwa dangon farko na shekarar 2026, musamman duba da cewa, sun hako danyen man da yawa a shekarar 2025.

Gazawar Nijeriya na hako yawan adadin danyen man, na ci gaba zama wata barazana gaga samarwa da kasar kudaden musaya na kasar waje musamman duba da cewa, fannin na hako danyen man, ya kasance daya daga cikin manyan hanyoyin samun kudaden shiga. Sai dai, wasu masana a fannin sun yi hasashen cewa, wannan ‘yar karuwar da aka samu ta hako danyen man, wata alama ce ta sake farfadowar fannin wanda kuma, dai kara karfafa samar da daidaito ga fannin.

Bugu da kari, kokarin da Gwamnatin Tarayya ke ci gaba da yi, na gyaran matatun mai mallakar ta da kuma kokarin janyo hankalin masu duba hannun jari ga fannin kamar irinsu Dangote, hakan, zai kara bunkasa fannin a shekarar 2026.

Hakazalika, wasu kwararru a fannin, na ganin ya zama wajibi a dauki matakan gaggawa kan batun magance matsalolin rashin tsaro da dakile masu fasa Bututun mai da samar da ingantattun kayan aiki,matukar ana son a samar da ci gaba mai dorewa ga fannin.

OPEC
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Ɗaura Ɗamarar Magance Matsalolin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Matatar Ɗangote Ta Ƙaryata Iƙirarin Dillalan Man Fetur 

MASU ALAKA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Next Post
Babu Wani Annabi Mai Daraja Kusa Da Ta Muhammad Rasulullah (SAW)

Babu Wani Annabi Mai Daraja Kusa Da Ta Muhammad Rasulullah (SAW)

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026
Xi Ya Yi Kira Da A Bunkasa Salon Zamanantarwa Na Sin Ta Hanyar Ingiza Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha

Xi Ya Yi Kira Da A Bunkasa Salon Zamanantarwa Na Sin Ta Hanyar Ingiza Kirkire-kirkiren Kimiyya Da Fasaha

July 8, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Kwankwaso Ya Mayar wa Ali Modu Sheriff Martani, Ya Ce Peter Obi Na da Gagarumin Goyon Baya a Arewa

July 8, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Waɗanda Aka Sace A Taraba

Sojoji Da NDLEA Sun Kama Mutanen Da Ake Zargi Da Kai wa ’Yan Ta’adda Miyagun Ƙwayoyi A Katsina

July 8, 2026
An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

An Gudanar Da Manyan Tarurruka 3 Game Da Kimiyya Da Fasaha A Beijing

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.