ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Jinjina Wa Tinubu Bisa Mayar Da Ofishin Ayyukan NPA Garin Warri

by Bello Hamza
9 months ago
Tinubu

Shugaban karamar hukumar Warri ta kudu kwamarde Agbateyiniro Isaac, ya yaba wa shugaban kasa Bola Tinubu, bisa umartar Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA na ta mayar da ofishin gudanar da ayyukan na hukumar zuwa yankin na Warri.

Agbateyiniro ya bayyana wannan matakin a matsayin abin kara karfafa kwarin guwai musamman ga yankin.

  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Farfesa Ibrahim Tsafe A Matsayin Sabon Shugaban Jami’ar ZAMSUT
  • Bunkasar Masana’antun Kasar Sin Ya Kai Kaso 6.0% a Watanni 11 Na Farkon Shekarar Bana

Kazalika, shugaban ya kuma godewa Gwamnan jihar Delta Sheriff Oborebwori, kan namijin kokari da ya yi, domin gknin an mayar da ofishin gudanar da ayyukan na hukumar zuwa yankin na Warri.

ADVERTISEMENT

Shugaba Agbateyiniro, wanda ya bayyana jin dadinsa kan mayar da ofishin gudanar da ayyukan na hukumar zuwa yankin na Warri ya sanar da cewa, wannan ci gaban da aka samu bisa kokarin da ake ci gaba da yi, a tsakanin Gwamnatin Tarayya da kuma jihar ta Delta musamman domin a kara habaka tattalin arziki a tsakanin Gwamnatin Tarayya da kuma ta jihar Delta.

Agbateyiniro, wanda ya yi wannan yabon a cikin sanarwar da ya fitar a garin Warri, ya kuma bayar da tabbacin cewaa karkashin shugabancin sa, a shirye ya ke, ya samar da kyakyawan yanayi ga mahukuntan hukumar ta NPA, domin ganin a cika wannan umarnin na shugaban kasa, ba tare da bata wani lokaci ba.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

Shugaban ya kuma yi kira ga nasu hada-hadar sufurin manyan motoci da ke gudanar da ayyukan su a yankin da sauran masu ruwa da tsaki da su yi amfani da wannan dsmar ta umarnin shugaban kasa.

“Wannan umarnin na shugaban kasa. tamkar bude wata kofa ce, da za ta kara taimaka wa, wajen kara bunkasa fannin tattalin arzikin karamar hukumar ta Warri, da kuma sauran sassan jihar ta Delta, Inji Agbateyiniro.

Kazalika, ya bayyana cewa, wannan damar, za ta kuma taimaka wajen samar da ayyukan yi ga alummar da ke a karamar hukumar ta Warri ta kudu wadda kuma za ta sanya, alummar jihar ta Delta, su kara amfana da tsare-tsaren da Gwamnan jihar Oborebwori ya kirkiro da su wanda hakan zai bai wa, ‘yan jihar, shiga cikin harkokin kasuwanci tare da kuma fitar da kayan da ake sarrawa a cikin jihar zuwa ketare.

Shugaban ya bayyana cewa, wannan umarnin, ya kuma kasance, tamkar samar da romon dimakariciyya ne, a karkashin shugabancin gwamnatin jami’iyyar APC.

“Ya zamar min dole in godewa gwamnan jihar Delta wanda kuma ya kasance Ubangi da na, a bangaren siyasamusamman saboda kammala ayyukan Gadojin Warri zuwa Ode da kuma ta zuwa Itsekiri da kuma aikin gyran hanya, da kudinsu ya kai na biliyoyin Naira, kammala wadannan ayyukan tabbas hakan ya nuna cewa, gwamnan mutum ne, mai cika alkarinsa,” A cewar shugaban.

Tinubu
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
Danyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.436 —OPEC

Danyen Mai Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Zuwa Ganga Miliyan 1.436 —OPEC

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.