• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mutane 12,000 Sun Sauya Sheka Daga PDP Zuwa APC A Kaduna

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Mutane 12,000 Sun Sauya Sheka Daga PDP Zuwa APC A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sama da ‘ya’yan jam’iyyar PDP 12,000 ne a karamar hukumar Giwa ta Jihar Kaduna suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki, tare da yin alkawarin mara wa jam’iyyar baya domin samun nasara a zaben 2023.

Wadanda suka sauya shekar da suka hada da tsohon kwamishina, shugabannin mata da matasa na jam’iyyar PDP a karamar hukumar Giwa, sun samu tarba daga shugaban jam’iyyar APC na jihar, Emmanuel Jakada da dan takarar gwamnan jam’iyyar, Sanata Uba Sani a wani gangami da aka gudanar a karamar hukumar.

  • Yawan Kayayyakin Da Masana’antu Sin Suka Samar Ya Karu Da Kaso 5 A Watan Oktoba
  • Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki

A jawabinsa na maraba, Sani ya ce zarge-zargen da ake yi wa jam’iyyar PDP a jihar a kullum, wata manuniya ce cewa nan ba da jimawa ba babbar jam’iyyar adawa za ta ruguje tun kafin babban zabe.

Ya kuma bai wa wadanda suka sauya shekar dama a jam’iyyar APC, ba tare da la’akari da sabbin mambobi ne su ba, ya kuma shawarce su da su yi aiki tare da kada kuri’a ga dukkan ‘yan takarar APC a zaben 2023.

“Mun gamsu cewa karamar hukumar Giwa za ta zabi jam’iyyarmu ta APC kuma PDP ta mutu a nan. Muna farin cikin sanar da ku cewa mambobin PDP 12,870 ne suka sauya sheka zuwa APC a yau. Muna so mu tabbatar muku da cewa dukkanku muna maraba da zuwa babbar jam’iyyarmu. Muna farin cikin sanar da ku cewa shugabar mata ta PDP ta dawo gare mu,” in ji Sani. ..

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

A nasa bangaren, shugaban jam’iyyar APC, Emmanuel Jakada, ya yaba wa sabbin ‘ya’yan jam’iyyar bisa sauya shekar da suka yi, inda ya ce jam’iyyar ta kawo ribar dimokuradiyya ga al’ummar Jihar Kaduna.

“Mun ji dadin yadda al’ummar karamar hukumar Giwa suka fahimci cewa babbar jam’iyyarmu ta APC ce aka fi aminta da su, muna godiya ga sabbin mambobinmu kuma za mu yi aiki da su, muna kara musu kwarin gwiwa don samun karin jama’a su shigo jam’iyyar mu. Mun yi imani, a 2023, za mu lashe dukkan mukamai, “in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCKadunaMembobiPDPSauya ShekatakaraUba SaniZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Addu’ar Tinubu Ga PDP Ya Nuna Alamun Nasara A Gare Mu – PDP

Next Post

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin Gwamnan APC A Taraba 

Related

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

24 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

2 days ago
Hoton Kwankwaso da Ganduje da Shekarau
Bakon Marubuci

Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar

3 days ago
Na Yafe Wa Buhari Duk Abin Da Ya Min – Buba Galadima
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

4 days ago
Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani
Manyan Labarai

Idan Jonathan Ya Tsaya Takara A 2027, Girmansa Zai Faɗi – Shehu Sani

4 days ago
PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke
Siyasa

PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke

5 days ago
Next Post
Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin Gwamnan APC A Taraba 

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin Gwamnan APC A Taraba 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.