• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mutane 12,000 Sun Sauya Sheka Daga PDP Zuwa APC A Kaduna

by Sadiq
3 years ago
in Siyasa
0
2023: Mutane 12,000 Sun Sauya Sheka Daga PDP Zuwa APC A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sama da ‘ya’yan jam’iyyar PDP 12,000 ne a karamar hukumar Giwa ta Jihar Kaduna suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki, tare da yin alkawarin mara wa jam’iyyar baya domin samun nasara a zaben 2023.

Wadanda suka sauya shekar da suka hada da tsohon kwamishina, shugabannin mata da matasa na jam’iyyar PDP a karamar hukumar Giwa, sun samu tarba daga shugaban jam’iyyar APC na jihar, Emmanuel Jakada da dan takarar gwamnan jam’iyyar, Sanata Uba Sani a wani gangami da aka gudanar a karamar hukumar.

  • Yawan Kayayyakin Da Masana’antu Sin Suka Samar Ya Karu Da Kaso 5 A Watan Oktoba
  • Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki

A jawabinsa na maraba, Sani ya ce zarge-zargen da ake yi wa jam’iyyar PDP a jihar a kullum, wata manuniya ce cewa nan ba da jimawa ba babbar jam’iyyar adawa za ta ruguje tun kafin babban zabe.

Ya kuma bai wa wadanda suka sauya shekar dama a jam’iyyar APC, ba tare da la’akari da sabbin mambobi ne su ba, ya kuma shawarce su da su yi aiki tare da kada kuri’a ga dukkan ‘yan takarar APC a zaben 2023.

“Mun gamsu cewa karamar hukumar Giwa za ta zabi jam’iyyarmu ta APC kuma PDP ta mutu a nan. Muna farin cikin sanar da ku cewa mambobin PDP 12,870 ne suka sauya sheka zuwa APC a yau. Muna so mu tabbatar muku da cewa dukkanku muna maraba da zuwa babbar jam’iyyarmu. Muna farin cikin sanar da ku cewa shugabar mata ta PDP ta dawo gare mu,” in ji Sani. ..

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

A nasa bangaren, shugaban jam’iyyar APC, Emmanuel Jakada, ya yaba wa sabbin ‘ya’yan jam’iyyar bisa sauya shekar da suka yi, inda ya ce jam’iyyar ta kawo ribar dimokuradiyya ga al’ummar Jihar Kaduna.

“Mun ji dadin yadda al’ummar karamar hukumar Giwa suka fahimci cewa babbar jam’iyyarmu ta APC ce aka fi aminta da su, muna godiya ga sabbin mambobinmu kuma za mu yi aiki da su, muna kara musu kwarin gwiwa don samun karin jama’a su shigo jam’iyyar mu. Mun yi imani, a 2023, za mu lashe dukkan mukamai, “in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCKadunaMembobiPDPSauya ShekatakaraUba SaniZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Addu’ar Tinubu Ga PDP Ya Nuna Alamun Nasara A Gare Mu – PDP

Next Post

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin Gwamnan APC A Taraba 

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

4 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

5 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

1 week ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin Gwamnan APC A Taraba 

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin Gwamnan APC A Taraba 

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.