• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mutane 12,000 Sun Sauya Sheka Daga PDP Zuwa APC A Kaduna

by Sadiq
2 years ago
in Siyasa
0
2023: Mutane 12,000 Sun Sauya Sheka Daga PDP Zuwa APC A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sama da ‘ya’yan jam’iyyar PDP 12,000 ne a karamar hukumar Giwa ta Jihar Kaduna suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki, tare da yin alkawarin mara wa jam’iyyar baya domin samun nasara a zaben 2023.

Wadanda suka sauya shekar da suka hada da tsohon kwamishina, shugabannin mata da matasa na jam’iyyar PDP a karamar hukumar Giwa, sun samu tarba daga shugaban jam’iyyar APC na jihar, Emmanuel Jakada da dan takarar gwamnan jam’iyyar, Sanata Uba Sani a wani gangami da aka gudanar a karamar hukumar.

  • Yawan Kayayyakin Da Masana’antu Sin Suka Samar Ya Karu Da Kaso 5 A Watan Oktoba
  • Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki

A jawabinsa na maraba, Sani ya ce zarge-zargen da ake yi wa jam’iyyar PDP a jihar a kullum, wata manuniya ce cewa nan ba da jimawa ba babbar jam’iyyar adawa za ta ruguje tun kafin babban zabe.

Ya kuma bai wa wadanda suka sauya shekar dama a jam’iyyar APC, ba tare da la’akari da sabbin mambobi ne su ba, ya kuma shawarce su da su yi aiki tare da kada kuri’a ga dukkan ‘yan takarar APC a zaben 2023.

“Mun gamsu cewa karamar hukumar Giwa za ta zabi jam’iyyarmu ta APC kuma PDP ta mutu a nan. Muna farin cikin sanar da ku cewa mambobin PDP 12,870 ne suka sauya sheka zuwa APC a yau. Muna so mu tabbatar muku da cewa dukkanku muna maraba da zuwa babbar jam’iyyarmu. Muna farin cikin sanar da ku cewa shugabar mata ta PDP ta dawo gare mu,” in ji Sani. ..

Labarai Masu Nasaba

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

A nasa bangaren, shugaban jam’iyyar APC, Emmanuel Jakada, ya yaba wa sabbin ‘ya’yan jam’iyyar bisa sauya shekar da suka yi, inda ya ce jam’iyyar ta kawo ribar dimokuradiyya ga al’ummar Jihar Kaduna.

“Mun ji dadin yadda al’ummar karamar hukumar Giwa suka fahimci cewa babbar jam’iyyarmu ta APC ce aka fi aminta da su, muna godiya ga sabbin mambobinmu kuma za mu yi aiki da su, muna kara musu kwarin gwiwa don samun karin jama’a su shigo jam’iyyar mu. Mun yi imani, a 2023, za mu lashe dukkan mukamai, “in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCKadunaMembobiPDPSauya ShekatakaraUba SaniZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

2023: Addu’ar Tinubu Ga PDP Ya Nuna Alamun Nasara A Gare Mu – PDP

Next Post

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin Gwamnan APC A Taraba 

Related

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

4 hours ago
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

2 days ago
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Siyasa

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

2 days ago
NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC
Siyasa

NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC

3 days ago
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu
Siyasa

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

4 days ago
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP
Siyasa

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

5 days ago
Next Post
Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin Gwamnan APC A Taraba 

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin Gwamnan APC A Taraba 

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.