ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki

by Sadiq
4 years ago
Sojoji

Rundunar Sojin Sama ta Operation Hadarin Daji ta kawar da wasu jiga-jigan ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo, Halilu Buzu, a Jihar Zamfara da Alhaji Ganai da abokinsa Yellow Kano a Jihar Kaduna. 

A cewar majiyae sojin, an kashe ‘yan ta’addan da mayakan ne a wasu hare-hare ta sama guda biyu biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu.

  • Yawan Adadin Mutane A Fadin Duniya Ya Doshi Mutum Biliyan 8 — MDD
  • 2023: Ko Takarar Gwamnan Kano Ta Yi Wa Sadiq Aminu Wali Girma?

An kashe Halilu Buzu ne a ranar 21 ga watan Oktoba, 2022 a yayin wani harin da aka kai musu ta sama a sansaninsu da ke karamar hukumar Maradun ta Jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT

Wani babban jami’i ya ce an ba da izinin kai harin ta sama ne bayan wasu bayanan sirri da aka samu sun nuna cewa wani kasurgumin dan ta’adda mai suna Halilu Buzu da ke garin Sububu a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara ya shirya ganawa da wasu daga cikin sojojin da ke yankin.

Hukumar leken asirin ta kuma bayyana inda da kuma ainihin wurin da yake ajiye kayan aikinsa inda shi da tawagarsa suka saba ajiye harsashi da ababen hawa.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

“Saboda haka, jiragen yaki NAF sun kai farmaki a lokaci guda inda taron ya gudana da kuma cibiyar hada kayan aiki.

“An hangi wata wuta ta tashi bayan kai harin, lamarin da ke nuni da cewa akwai yuwuwar wurin ya kunshi wani abu mai zafi,” in ji jami’in.

Majiyar ta ce binciken da aka yi a kan barnar shanu ya nuna wurin da taron ya gudana da kuma wurin da aka a lalata.

Ya ce bayanan da aka samu a baya-bayan nan sun nuna cewa lallai an kawar da Halilu Buzu a harin da aka kai ta sama tare da wasu shugabannin ‘yan ta’adda.

Ya kara da cewa, “Kawar da Halilu Buzu ya zo ne a matsayin abun farin ciki ga mazauna yankin Sububu, Anka (Bayan Daji) da kuma mahadar Bayan Ruwa a Jihar Zamfara bisa la’akari da kwarewarsa wajen ta’addanci da azabtar da wadanda yake yin garkuwa da su, tuni rashinsa ya rage yawaitar faruwar kai hare-hare da garkuwa da mutane, satar shanu da sauran ayyukan ta’addanci a yankin.”

Ya ce an kai irin wannan harin ta sama a ranar 14 ga watan Nuwamba, 2022 a wani wurin da wani kasurgumin dan ta’adda yake a unguwar Alhaji Ganai a dajin Kidandan da ke karamar hukumar Giwa a Jihar Kaduna.

Ya ce harin ta sama ya zama wajibi ne bayan da hukumar leken asiri ta sa ido da bin diddigi, da kuma gano yadda al’amuran Alhaji Ganai da dakarunsa ke a wurin.

“Bayanan sirri sun nuna cewa an lalata wasu gine-ginen da ke wurin da suka hada da gidan Alhaji Ganai da babura, sannan an kashe ‘yan ta’adda da dama da suka hada da Yello Kano, na hannun damar shugaban ‘yan ta’adda, Musa Balejo da wasu kasurguman ‘yan ta’adda bakwai bayan harin,” a cewarsa.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

Kyautata Alakar Sin Da Amurka Na Iya Shawo Kan Matsalolin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.