ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Mutane 12,000 Sun Sauya Sheka Daga PDP Zuwa APC A Kaduna

by Sadiq
4 years ago
APC

Sama da ‘ya’yan jam’iyyar PDP 12,000 ne a karamar hukumar Giwa ta Jihar Kaduna suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki, tare da yin alkawarin mara wa jam’iyyar baya domin samun nasara a zaben 2023.

Wadanda suka sauya shekar da suka hada da tsohon kwamishina, shugabannin mata da matasa na jam’iyyar PDP a karamar hukumar Giwa, sun samu tarba daga shugaban jam’iyyar APC na jihar, Emmanuel Jakada da dan takarar gwamnan jam’iyyar, Sanata Uba Sani a wani gangami da aka gudanar a karamar hukumar.

  • Yawan Kayayyakin Da Masana’antu Sin Suka Samar Ya Karu Da Kaso 5 A Watan Oktoba
  • Sojoji Sun Kashe Shugabannin ‘Yan Bindiga Buzu, Ganai Da sauransu A Harin Jirgin Yaki

A jawabinsa na maraba, Sani ya ce zarge-zargen da ake yi wa jam’iyyar PDP a jihar a kullum, wata manuniya ce cewa nan ba da jimawa ba babbar jam’iyyar adawa za ta ruguje tun kafin babban zabe.

ADVERTISEMENT

Ya kuma bai wa wadanda suka sauya shekar dama a jam’iyyar APC, ba tare da la’akari da sabbin mambobi ne su ba, ya kuma shawarce su da su yi aiki tare da kada kuri’a ga dukkan ‘yan takarar APC a zaben 2023.

“Mun gamsu cewa karamar hukumar Giwa za ta zabi jam’iyyarmu ta APC kuma PDP ta mutu a nan. Muna farin cikin sanar da ku cewa mambobin PDP 12,870 ne suka sauya sheka zuwa APC a yau. Muna so mu tabbatar muku da cewa dukkanku muna maraba da zuwa babbar jam’iyyarmu. Muna farin cikin sanar da ku cewa shugabar mata ta PDP ta dawo gare mu,” in ji Sani. ..

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

A nasa bangaren, shugaban jam’iyyar APC, Emmanuel Jakada, ya yaba wa sabbin ‘ya’yan jam’iyyar bisa sauya shekar da suka yi, inda ya ce jam’iyyar ta kawo ribar dimokuradiyya ga al’ummar Jihar Kaduna.

“Mun ji dadin yadda al’ummar karamar hukumar Giwa suka fahimci cewa babbar jam’iyyarmu ta APC ce aka fi aminta da su, muna godiya ga sabbin mambobinmu kuma za mu yi aiki da su, muna kara musu kwarin gwiwa don samun karin jama’a su shigo jam’iyyar mu. Mun yi imani, a 2023, za mu lashe dukkan mukamai, “in ji shi.

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin Gwamnan APC A Taraba 

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin Gwamnan APC A Taraba 

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.