• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

by Khalid Idris Doya
4 months ago
in Labarai
0
2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanaki kalilan da shiga sabuwar shekarar 2025, sabbin hare-haren ‘yan ta’adda, ‘yan fashin daji da sauran ayyukan ta’addanci ya zama wani abu na tura razani a zukatan al’umma a sassa daban-daban na kasar nan.

A cewar rahotanni, sama da mutum 78 ne aka kashe, yayin da kuma aka yi garkuwa da wasu mutum 80 a sassan jihohi daban-daban a mako na farko na watan Janairun 2025.

  • Ranar Tunawa Da Mazan Jiya: Gwamna Lawal Ya Yi AlÆ™awarin Inganta Rayuwar Iyalan Jaruman Da Suka Rasu
  • Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 – NBS

A ranar Asabar 4 ga Janairu, kusan sojoji takwas aka kashe a lokacin da ‘yan ta’adda suka kai hari a sansanin sojoji da ke Sabon Gari a karamar hukumar Dambo ta Jihar Borno.

Kazalika, ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Argungu da ke Jihar Kebbi, inda suka kashe mutum biyu, lamarin da kakakin ‘yansandan Jihar Kebbi, Nafiu Abubakar ya tabbatar da faruwarsa.

Wani karin abun takaici shi ne, yadda aka samun labarin kai hari a Charanci, Safana, Kurfi, da karamar hukumar Kaita a jihar Katsina, inda aka kashe sama da mutum 30 a tsakanin ranar Talata zuwa Alhamis.

Labarai Masu Nasaba

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

An labarto cewa ‘yan bindiga ne suka farmaki mutanen a lokacin da suke dawowa daga ta’aziyya a karamar hukumar Batsari.

Haka kuma, ‘yan fashin daji sun kaddamar da munanan hare-hare a Jihar Borno da Kebbi, sannan wasu ‘yan bindiga da ba gano su waye ba da ke sheke ayarsu a yankin Umuokanne da ke Jihar Imo sun kashe mutane uku.

‘Yan awannin da harin Umuokanne, wasu ‘yan bindiga sun kaddamar da wani mummunar hari a Orsu ta Jihar Imo, inda mutum 18 suka rasa rayukansu.

A wani labarin kuma, wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan kungiyar ta’addan Lakurawa ne sun kashe ma’aikatan kamfanin Airtel guda biyu da wani mazaunin kauyen Gumki da ke karamar hukumar Arewa ta Jihar Kebbi a karshen mako.

An tattaro cewa ‘yan ta’addan sun mamaye al’ummar da ke tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, bayan da suka samu labarin cewa kamfanin sadarwa na kafa wata kafa ta sa ido a yankin.

Wasu mutane 11 kuma aka kashe a kauyen Gululu da ke Jahun da Miga. Sannan a ranar Laraba 8 ga Janairu, ‘yan bindiga sun mamaye kauyen Idu da ke gundumar Kufana a karamar hukumar Kajuru tare da kashe mutum 2. A kuma wannan ranar an kashe jami’ai guda 2 a wani harin da ‘yan Boko Haram suka kai a caji ofis din ‘yansanda da ke Borno.

Haka zalika, an ruwaito cewa wasu ‘yan bindiga sun kashe wani manomi mai suna Terzungwe Shaku a kauyen Akor da ke karamar hukumar Guma a Jihar Benuwai.

Shaku, wanda kuma ya mallaki wurin shan giya a kasuwar Akor, an sace shi ne jim kadan kafin sabuwar shekara kuma aka yi garkuwa da shi sama da makonni biyu kafin a kashe shi.

Mazauna yankin sun ce da farko masu garkuwa da mutanen sun bukaci naira miliyan 20, amma dangin sun tattauna kan naira miliyan 5.4, inda suka amince kuma iyalan suka biya.

Mutane da dama ne suka biya kudin fansa domin ceto ‘yan uwansu daga garkuwar da ‘yan bindiga suka yi wa ‘yan uwansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FargabaGarkuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

SIMDA Ta Ƙulla Alaƙa Da Jami’ar Skyline Kan Ci Gaban Ilimi Da Kasuwancin Zamani A Kano

Next Post

Lokacin Ya Yi Na Fahimtar Ainihin Kasar Sin

Related

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
Labarai

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

1 hour ago
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa
Labarai

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

2 hours ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

3 hours ago
Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU
Labarai

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

3 hours ago
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
Labarai

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

4 hours ago
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar
Manyan Labarai

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

8 hours ago
Next Post
Lokacin Ya Yi Na Fahimtar Ainihin Kasar Sin

Lokacin Ya Yi Na Fahimtar Ainihin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

May 11, 2025
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

May 11, 2025
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

May 11, 2025
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

May 11, 2025
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

May 11, 2025
Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

May 11, 2025
Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

May 11, 2025
Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.