• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

by Khalid Idris Doya
10 months ago
Fargaba

Kwanaki kalilan da shiga sabuwar shekarar 2025, sabbin hare-haren ‘yan ta’adda, ‘yan fashin daji da sauran ayyukan ta’addanci ya zama wani abu na tura razani a zukatan al’umma a sassa daban-daban na kasar nan.

A cewar rahotanni, sama da mutum 78 ne aka kashe, yayin da kuma aka yi garkuwa da wasu mutum 80 a sassan jihohi daban-daban a mako na farko na watan Janairun 2025.

  • Ranar Tunawa Da Mazan Jiya: Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Inganta Rayuwar Iyalan Jaruman Da Suka Rasu
  • Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 – NBS

A ranar Asabar 4 ga Janairu, kusan sojoji takwas aka kashe a lokacin da ‘yan ta’adda suka kai hari a sansanin sojoji da ke Sabon Gari a karamar hukumar Dambo ta Jihar Borno.

Kazalika, ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Argungu da ke Jihar Kebbi, inda suka kashe mutum biyu, lamarin da kakakin ‘yansandan Jihar Kebbi, Nafiu Abubakar ya tabbatar da faruwarsa.

Wani karin abun takaici shi ne, yadda aka samun labarin kai hari a Charanci, Safana, Kurfi, da karamar hukumar Kaita a jihar Katsina, inda aka kashe sama da mutum 30 a tsakanin ranar Talata zuwa Alhamis.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

An labarto cewa ‘yan bindiga ne suka farmaki mutanen a lokacin da suke dawowa daga ta’aziyya a karamar hukumar Batsari.

Haka kuma, ‘yan fashin daji sun kaddamar da munanan hare-hare a Jihar Borno da Kebbi, sannan wasu ‘yan bindiga da ba gano su waye ba da ke sheke ayarsu a yankin Umuokanne da ke Jihar Imo sun kashe mutane uku.

‘Yan awannin da harin Umuokanne, wasu ‘yan bindiga sun kaddamar da wani mummunar hari a Orsu ta Jihar Imo, inda mutum 18 suka rasa rayukansu.

A wani labarin kuma, wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan kungiyar ta’addan Lakurawa ne sun kashe ma’aikatan kamfanin Airtel guda biyu da wani mazaunin kauyen Gumki da ke karamar hukumar Arewa ta Jihar Kebbi a karshen mako.

An tattaro cewa ‘yan ta’addan sun mamaye al’ummar da ke tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, bayan da suka samu labarin cewa kamfanin sadarwa na kafa wata kafa ta sa ido a yankin.

Wasu mutane 11 kuma aka kashe a kauyen Gululu da ke Jahun da Miga. Sannan a ranar Laraba 8 ga Janairu, ‘yan bindiga sun mamaye kauyen Idu da ke gundumar Kufana a karamar hukumar Kajuru tare da kashe mutum 2. A kuma wannan ranar an kashe jami’ai guda 2 a wani harin da ‘yan Boko Haram suka kai a caji ofis din ‘yansanda da ke Borno.

Haka zalika, an ruwaito cewa wasu ‘yan bindiga sun kashe wani manomi mai suna Terzungwe Shaku a kauyen Akor da ke karamar hukumar Guma a Jihar Benuwai.

Shaku, wanda kuma ya mallaki wurin shan giya a kasuwar Akor, an sace shi ne jim kadan kafin sabuwar shekara kuma aka yi garkuwa da shi sama da makonni biyu kafin a kashe shi.

Mazauna yankin sun ce da farko masu garkuwa da mutanen sun bukaci naira miliyan 20, amma dangin sun tattauna kan naira miliyan 5.4, inda suka amince kuma iyalan suka biya.

Mutane da dama ne suka biya kudin fansa domin ceto ‘yan uwansu daga garkuwar da ‘yan bindiga suka yi wa ‘yan uwansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Next Post
Lokacin Ya Yi Na Fahimtar Ainihin Kasar Sin

Lokacin Ya Yi Na Fahimtar Ainihin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.