• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

by Khalid Idris Doya
7 months ago
in Labarai
0
2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanaki kalilan da shiga sabuwar shekarar 2025, sabbin hare-haren ‘yan ta’adda, ‘yan fashin daji da sauran ayyukan ta’addanci ya zama wani abu na tura razani a zukatan al’umma a sassa daban-daban na kasar nan.

A cewar rahotanni, sama da mutum 78 ne aka kashe, yayin da kuma aka yi garkuwa da wasu mutum 80 a sassan jihohi daban-daban a mako na farko na watan Janairun 2025.

  • Ranar Tunawa Da Mazan Jiya: Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Inganta Rayuwar Iyalan Jaruman Da Suka Rasu
  • Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 – NBS

A ranar Asabar 4 ga Janairu, kusan sojoji takwas aka kashe a lokacin da ‘yan ta’adda suka kai hari a sansanin sojoji da ke Sabon Gari a karamar hukumar Dambo ta Jihar Borno.

Kazalika, ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Argungu da ke Jihar Kebbi, inda suka kashe mutum biyu, lamarin da kakakin ‘yansandan Jihar Kebbi, Nafiu Abubakar ya tabbatar da faruwarsa.

Wani karin abun takaici shi ne, yadda aka samun labarin kai hari a Charanci, Safana, Kurfi, da karamar hukumar Kaita a jihar Katsina, inda aka kashe sama da mutum 30 a tsakanin ranar Talata zuwa Alhamis.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

An labarto cewa ‘yan bindiga ne suka farmaki mutanen a lokacin da suke dawowa daga ta’aziyya a karamar hukumar Batsari.

Haka kuma, ‘yan fashin daji sun kaddamar da munanan hare-hare a Jihar Borno da Kebbi, sannan wasu ‘yan bindiga da ba gano su waye ba da ke sheke ayarsu a yankin Umuokanne da ke Jihar Imo sun kashe mutane uku.

‘Yan awannin da harin Umuokanne, wasu ‘yan bindiga sun kaddamar da wani mummunar hari a Orsu ta Jihar Imo, inda mutum 18 suka rasa rayukansu.

A wani labarin kuma, wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan kungiyar ta’addan Lakurawa ne sun kashe ma’aikatan kamfanin Airtel guda biyu da wani mazaunin kauyen Gumki da ke karamar hukumar Arewa ta Jihar Kebbi a karshen mako.

An tattaro cewa ‘yan ta’addan sun mamaye al’ummar da ke tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, bayan da suka samu labarin cewa kamfanin sadarwa na kafa wata kafa ta sa ido a yankin.

Wasu mutane 11 kuma aka kashe a kauyen Gululu da ke Jahun da Miga. Sannan a ranar Laraba 8 ga Janairu, ‘yan bindiga sun mamaye kauyen Idu da ke gundumar Kufana a karamar hukumar Kajuru tare da kashe mutum 2. A kuma wannan ranar an kashe jami’ai guda 2 a wani harin da ‘yan Boko Haram suka kai a caji ofis din ‘yansanda da ke Borno.

Haka zalika, an ruwaito cewa wasu ‘yan bindiga sun kashe wani manomi mai suna Terzungwe Shaku a kauyen Akor da ke karamar hukumar Guma a Jihar Benuwai.

Shaku, wanda kuma ya mallaki wurin shan giya a kasuwar Akor, an sace shi ne jim kadan kafin sabuwar shekara kuma aka yi garkuwa da shi sama da makonni biyu kafin a kashe shi.

Mazauna yankin sun ce da farko masu garkuwa da mutanen sun bukaci naira miliyan 20, amma dangin sun tattauna kan naira miliyan 5.4, inda suka amince kuma iyalan suka biya.

Mutane da dama ne suka biya kudin fansa domin ceto ‘yan uwansu daga garkuwar da ‘yan bindiga suka yi wa ‘yan uwansu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FargabaGarkuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

SIMDA Ta Ƙulla Alaƙa Da Jami’ar Skyline Kan Ci Gaban Ilimi Da Kasuwancin Zamani A Kano

Next Post

Lokacin Ya Yi Na Fahimtar Ainihin Kasar Sin

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

3 minutes ago
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

1 hour ago
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano
Labarai

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

3 hours ago
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

6 hours ago
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Labarai

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

7 hours ago
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe
Labarai

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

8 hours ago
Next Post
Lokacin Ya Yi Na Fahimtar Ainihin Kasar Sin

Lokacin Ya Yi Na Fahimtar Ainihin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Kafa Sabbin Manyan Makarantu Na Tsawon Shekaru 7

August 13, 2025
Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

August 13, 2025
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

August 13, 2025
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.