• English
  • Business News
Friday, August 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
3 weeks ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

LEADERSHIP ta ruwaito cewa masu neman takarar shugaban kasa a karkashin hadakar jam’iyyar ADC za su sanya hannu a kan yarjejeniyar tallafa wa duk wanda ya zama dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.

Wannan yarjejeniya ce da ‘yan takara suka cimma, amma duk da haka, dole ne su gudanar da zaben fid da gwani a tsakaninsu.

  • Akwai Bukatar Daina Cin Zarafin Malaman Makaranta
  • Nazari Game Da Rayuwar Muhammadu Buhari

Tsohon ministan sufuri da kuma babban jigo a hadakar jam’iyyar, Rotimi Amaechi, ya bayyana wa LEADERSHIP hakan yayin wata tattaunawa da shi.

Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar, Sanata Dabid Mark, ya bayyana cewa jam’iyyar ba ta da wanda ta fi so a matsayin dan takara kuma ya tabbatar da cewa a karkashin shugabancinsa, jam’iyyar za ta kai ga nasara.

Mark ya yi wannan bayani ne a daidai lokacin da wasu manyan mambobin hadin gwiwa suke matsa kaimi kan neman tikitin takarar shugaban kasa a jam’iyyar.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya bayyana burinsa na tsayawa takara a 2027, yayin da yake karban bakuncin tawagar masu ruwa da tsaki daga Gombe a gidansa da ke Abuja a ranar Asabar da ta gabata. Daga bisani, ya musanta cewa ya halarci wani taron da aka matsa masa lamba don ya janye kudirinsa na takara ga yankin kudu.

Haka shi ma, tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi, ya bayyana kudirinsa na tsayawa takarar shugaban kasa, yana mai cewa bai tattaunawa da kowa don ya zama dan takarar mataimakin shugaban kasa a 2027 ba.

Yayin da magoya bayan ‘yan takarar shugaban kasan guda biyu da suka tsaya takara tare a 2019 ke karfafa gwiwar fitowar takarar shugaban kasar Nijeriya, musamman a shafukan sada zumunta, tsohon ministan sufuri, Chibuike Amaechi, shi ma ya bayyana aniyarsa ta sake yin takara a zaben shugaban kasa a 2027 karkashin tutar jam’iyyar ADC.

Ya taba takarar shugaban kasa bai samu nasara ba a jam’iyyar APC a 2023, wanda Shugaba Bola Tinubu ya doke shi a zaben fid da gwani. Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya bayyana a cikin wata hira cewa ba ya da burin za ma shugaban kasa a halin yanzu.

Amma shi kuwa tsohon dan takarar shugaban kasa na ADC, Dumebi Kachikwu, ya zargi cewa jam’iyyar a karkashin sabuwar jagoranci, tana shirin ba da tikitin ta ga dan arewa, musamman ga Atiku.

Ya yi wannan zargin ne a daidai lokacin da ake zazzafar muhawara kan bayar da takarar shugaban kasa a yankin kudu ko arewa.

Wannan muhawara ta kasance daya daga cikin muhimman abubuwan da suka shafi zaben shugaban kasa na 2023 wanda Shugaban kasa Bola Tinubu na APC ya lashe, wanda ya sanya tikiti ya koma yankin kudanci bayan mulkin shekaru takwas na shugaban kasa Muhammadu Buhari daga arewa.

Da yake zantawa da LEADERSHIP, Amaechi ya bayyana cewa yarjejeniyar tallafa wa duk wanda ya samu nasarar zama dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar za ta maida hankali ne kan fahimtar juna game da abin da za a kira gudanar sahihin zaben fid da gwani.

Tsohon gwamnan Jihar Ribas ya ce, “Abin da muka yarda a zahiri shi ne, dole ne in ce akwai bukatar a bayyana al’amarin abin da muka yarda shi ne na cewa duk wanda ya zama dan takarar shugaban kasa bisa yadda aka gudanar da sahihin zaben fid da gwani, to dole ne dukkanmu mu mara masa baya.

“Abu na farko shi ne, dole ne mu zauna mu fayyace abin da muke nufi da sahihin zaben fid da gwani, saboda yana da sauki ga wani ya sauya tsarin kuma ya kira shi da suna sahihin zaben fid da gwani,” in ji shi.

Kazalika, sakataren yada labarai na ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya shaida wa LEADERSHIP cewa ba ya san da irin wannan yarjejeniyar ba.

Sakataren yada labaran jam’iyyar ya ce duk da haka jam’iyyar za ta yi iya bakin kokarinta wajen yi wa masu neman takara adalci a dukkan wani mataki.

Bolaji ya ce, “Ba na da masaniya game da wani yarjejeniya a tsakanin ‘yan takara. Abin da jam’iyya ta kudiri niyya shi ne, samar da kyawawan yanayi ga wani dan takara tare da yin adalci a tsananinsu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Next Post

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

2 weeks ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

4 weeks ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

4 weeks ago
Next Post
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

Barcelona Ta Tube Ter Stergen Daga Mukaminsa Na Kaftin Din Kungiyar 

August 7, 2025
Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

August 7, 2025
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 7, 2025
Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

Cinikayyar Kayayyaki a Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.5 Cikin 100 Cikin Watanni 7 Na Farkon Shekarar Nan

August 7, 2025
Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

August 7, 2025
Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas 

August 7, 2025
Neja

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago

August 7, 2025
Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza

August 7, 2025
Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama

August 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.