• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

4 Daga Cikin Masallatan Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Kaduna Sun Bar Marayu Da Zawarawa 61

by Khalid Idris Doya
2 years ago
'Yan Bindiga

Mutum hudu daga cikin wadanda ‘yan bindiga suka harbe a cikin masallaci a Kaduna sun bar iyalai da zawarawa 61 kamar yadda jaridar Daily Trust ta nakalto.

Idan za ku tuna dai wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun farmaki masallata a masallacin Saya-Saya da ke karamar hukumar Ikara a jihar Kaduna tare da kashe mutum bakwai a daren ranar Juma’ar da ta gabata.

  • SERAP Ta Maka Tinubu A Kotu Kan Haramta Wa ‘Yan Jarida 25 Dauko Rahotonni A Fadar Shugaban Kasa

‘Yan bindigar sun kai farmakin ne  a kan Babura inda suka farmaki mutane da ke sallah acikin Masallacin, hakan ya basu damar kashewa da jikkata wasu da ke ibadar sannan daga bisani suka arce.

Wani tsohon manomi kuma dan kasuwa, Ya’u Ibrahim, wanda ke da ‘ya’ya 20 da mata biyu na daga cikin wadanda ‘yan bindigan suka kashe a wannan harin.

Sauran sun hada da kwamandan ‘yan banga na JTF wanda ake kyautata tsammanin shi ‘yan bindigar ke farauta, Malam Isiaka, wanda ya rasu yana da ‘ya’ya 17 da mata uku.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

Kazalika, wani mazaunin kauyen, Yunusa Nuhu, an kasheshi ya bar ‘ya’ya 14 da mata biyu, yayin da kuma Malam Adamu na Gidan Maidara ya bar ‘ya’ya 10.

Malam Dan Asabe Saya-saya, sarkin kauyen, ya nuna harin a matsayin abun takaici da damuwa matuka.

Ya bayyana cewar wani Mustapha Sale, dan shekara 25 a duniya, shi ne kawai daga cikin wadanda aka kashe din bai da mata.

“Kamar yadda kuka sani, mutum biyar a cikin masallacin kauyen aka kashe su, yayin da aka kashe wasu hudu kuma a kauyukan da ke makwafta. sannan, hudu daga cikin wanda aka kashe sun bar duniya da ‘ya’ya da mata 61,” ya shaida.

“Mutum daya ne kawai bai da aure, kuma shi ma an riga an gama shirye-shiryen aurensa wannan harin ya rutsa da shi.”

Ya ce, iyalan mamatan suna tsananin bukatar tallafi da taimako a halin yanzu domin yadda za su iya rike kansu da ‘ya’yansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi
Manyan Labarai

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Kubutar Da Mutum 3 Daga Harin ‘Yan Fashin Daji A Jihar Kaduna

'Yansanda Sun Kubutar Da Mutum 3 Daga Harin 'Yan Fashin Daji A Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Radda

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Al’umma Su Hada Hannu Da Gwamnati Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
IMF

Fitar Da Kudi Ta Haramtacciyar Hanya Na Kara Dagula Matsalar Tattalin Arziki – IMF

October 18, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.