ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

4 Daga Cikin Masallatan Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Kaduna Sun Bar Marayu Da Zawarawa 61

by Khalid Idris Doya
3 years ago
'Yan Bindiga

Mutum hudu daga cikin wadanda ‘yan bindiga suka harbe a cikin masallaci a Kaduna sun bar iyalai da zawarawa 61 kamar yadda jaridar Daily Trust ta nakalto.

Idan za ku tuna dai wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun farmaki masallata a masallacin Saya-Saya da ke karamar hukumar Ikara a jihar Kaduna tare da kashe mutum bakwai a daren ranar Juma’ar da ta gabata.

  • SERAP Ta Maka Tinubu A Kotu Kan Haramta Wa ‘Yan Jarida 25 Dauko Rahotonni A Fadar Shugaban Kasa

‘Yan bindigar sun kai farmakin ne  a kan Babura inda suka farmaki mutane da ke sallah acikin Masallacin, hakan ya basu damar kashewa da jikkata wasu da ke ibadar sannan daga bisani suka arce.

ADVERTISEMENT

Wani tsohon manomi kuma dan kasuwa, Ya’u Ibrahim, wanda ke da ‘ya’ya 20 da mata biyu na daga cikin wadanda ‘yan bindigan suka kashe a wannan harin.

Sauran sun hada da kwamandan ‘yan banga na JTF wanda ake kyautata tsammanin shi ‘yan bindigar ke farauta, Malam Isiaka, wanda ya rasu yana da ‘ya’ya 17 da mata uku.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Kazalika, wani mazaunin kauyen, Yunusa Nuhu, an kasheshi ya bar ‘ya’ya 14 da mata biyu, yayin da kuma Malam Adamu na Gidan Maidara ya bar ‘ya’ya 10.

Malam Dan Asabe Saya-saya, sarkin kauyen, ya nuna harin a matsayin abun takaici da damuwa matuka.

Ya bayyana cewar wani Mustapha Sale, dan shekara 25 a duniya, shi ne kawai daga cikin wadanda aka kashe din bai da mata.

“Kamar yadda kuka sani, mutum biyar a cikin masallacin kauyen aka kashe su, yayin da aka kashe wasu hudu kuma a kauyukan da ke makwafta. sannan, hudu daga cikin wanda aka kashe sun bar duniya da ‘ya’ya da mata 61,” ya shaida.

“Mutum daya ne kawai bai da aure, kuma shi ma an riga an gama shirye-shiryen aurensa wannan harin ya rutsa da shi.”

Ya ce, iyalan mamatan suna tsananin bukatar tallafi da taimako a halin yanzu domin yadda za su iya rike kansu da ‘ya’yansu.

'Yan Bindiga
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Kubutar Da Mutum 3 Daga Harin ‘Yan Fashin Daji A Jihar Kaduna

'Yansanda Sun Kubutar Da Mutum 3 Daga Harin 'Yan Fashin Daji A Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.