• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Halascin Yanke Farce Ko Aski Ga Wanda Ya Yi Niyyar Layya

by Najibullah Mohammed
11 months ago
in Addini
0
Halascin Yanke Farce Ko Aski Ga Wanda Ya Yi Niyyar Layya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yin aski ko yanke farce a goman farko na Zulhijja ba ya hana yin layya ko idan an yi ta zama karbabbiya ko ingantacciya, muddin mai layya ya cika sharuddan da shari’a ta ajiye a kan yin layyarsa, akwai sharudda a kan kansa, akwai sharudda akan layyarsa, akwai kuma sharudda akan dabbar.

Sharudda a kansa ya zama yana da iko na yin layyar, yanka kuma wajibi ne a yi ranar sallah bayan limamin da yake masu salla a garinsu ko a unguwarsu ya yanka dabbarsa, ko kuma ya bada izini kowa ya yanka layyarsa,duk wanda ya yanka dabbarsa kafin liman ya yanka tashi yankansa bai yiwu ba, ita kuma dabbar da za a yanka lallai ne ta zama daga cikin dabbobin ni’ima, wato Rakuma, Shanu, Tumakai da Awakai, kuma lallai ne dabbar ta zama ta cika shekarun girma jinsinta, kuma ba ta da nakasa ko wata illa kamar makanta ko gurguntaka ko rauni wanda yake fitar da jini bai warke ba.Muddin an cika wa’dannan sharuddan aka yi yankan nan to layya ta yi. Yin askin mai layya ko yanke farcensa bai shafi ingantuwar layyarsa ba ko rashin ingantuwarta.

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Inganta Tsarin Kamfanoni Na Zamani Mai Halayyar Musamman Ta Sin
  • Layya Babbar Ibada A Musulunci Na 4

Da yawa mutane su na daukar hadisin uwar Muminai Nana Ummu Salama wacce ta rawaito cewa; Annabi (SAW) ya ce, idan watan Zulhijja ya kama duk wanda yake da abin yanka wanda zai yanka a matsayin layya to kada ya yi aski ko yanke farce a wadannan kwanuka har sai ya yi layyarsa. Wannan hadisi an ganshi a cikin littafin Imamu Muslim.

Abinda muke jan hankalin mutane a kansa, litattafan hadisai musamman su manyan litattafai wato irinsu Bukhari da Muslim da sauransu abin da suka shardanta wa kansu cewa za su kawo dukkan hadisan da suka inganta cewa Annabi (SAW) ya fade su, amma ba su dora wa kansu ba yi wa mutane bayanin cewa wannan hadisi har yanzu yana aiki ko ba ya aiki, ko wannan hadisi akwai wani hadisin da ya dakatar da aikinsa ko ya rage fadin aikinsa ko ya kara fadin aikinsa, su dai kawai su na kawo hadisai ne ingantattu daga Annabi (SAW). Ba za ka iya gane cewa wannan hadisi har yanzu yana aiki ko ba ya aiki ba ko mene ne fadin ma’anarsa, ko me ake nufi da shi sai ka koma wajen malamai masana su ne za su yi ma wannan bayanin.

Kamar yadda a Alkur’ani za ka iya samun ayoyi tuli wadanda ga su nan har yanzu Alkur’ani ne ana karanta su amma kuma aiki da su an dakatar da shi. Bari mu ba da misalin guda daya. Fadin Allah (SWT) da yake cewa; Sura: 2 aya: 234, “Duk wadanda suka mutu daga cikinku suka bar matansu, matan za su zauna har tsawon wata hudu da kwana goma kafin su yi aure (wato zaman takaba ke nan).”

Labarai Masu Nasaba

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

An Gano Cushen Biliyan 5 Cikin Kasafin Kuɗin Hukumar Alhazai Ta Ƙasa

Sai ga wata aya ita kuma a cikin dai wannan sura: 2, aya: 240; Allah yana cewa; “Wadanda suka mutu daga cikinku suka bar mata ana ba matansu umarni zama tsawon shekara guda ba tare da fita ba kafin su yi aure.”

Dukkan wadannan ayoyi guda biyu ayoyi ne na Alkur’ani kuma har gobe ana karanta su,amma daya ta warware hukuncin daya, saboda haka dole ne daya za a dauka daga ciki, ba za a yi amfani da dayar ba.

Irin wadannan misalai suna da yawa a cikin Alkur’ani da hadisan Annabi (SAW). Shi ya sa wannan hadisi da muka fada a sama na uwar Muminai Ummu Salama Allah ya yarda da ita, hadisin Nana A’isha uwar Muminai Allah ya yarda da ita ya warware shi, inda take cewa;

Ita ce take shirya dabaibayi da igiyar daure dabbobin da Manzon Allah (SAW) zai yi layya da su ya aika su zuwa Harami, idan ya yi haka Annabi (SAW) bai taba hana kansa wani abu da Allah ya halatta mashi ba saboda dalilin ya yi niyyar zai yi layya. Shi ma dai wannan hadisi Imamu Muslim ne har yau ya rawaito shi, ta yadda za ka gane cewa Imamu Muslim yana kawo hadisai ne da suka inganta daga Annabi (SAW) ba yana aikin cewa wannan ana aiki da shi ko wannan ba a aiki da shi ba, kamar yadda aka rawaito hadisin da Annabi (SAW) aka tambaye shi a kan hukuncin wanda ya shafi azzakarinsa bayan ya yi alwala, Annabi (SAW) ya ba da amsar cewa azzakari wani bangare ne na jikin mutum saboda haka don mutum ya shafe shi alwalarsa tana nan, sai kuma ga wani hadisi shi kuma Annabi (SAW) yana cewa; Duk wanda ya shafi azzakarinsa bayan ya yi alwala to ya sake yin alwala.

Su ma wadannan hadisai guda biyu dukkansu Imamu Hajar Al-Askalani ya kawo su a cikin Albulugul Maram.

Saboda haka muke jan hankalin mutane da cewa yin aski ko yanke farce bai shafi hukuncin layya ba, ingancinta ko rashin ingancinta ba, suna nan a kan hukuncinsu. Akwai wasu malamai wadanda suke nuna cewa yin aski ko yanke farce dama ce ta mutum idan yana so ya yi idan kuma ba ya so sai ya bar shi, saboda ganin cewa idan an zo lissafa ladan da zai samu idan ya yi layya za a lissafa dukkan kwayar gashi da ta ke jikinsa, to idan ya aske su wai ba za a lissafa da su ba. To amma shi gashi ranar da aka aske shi washegari ma fitowa yake yi kuma wannan ba zai sa a ki lissafawa da shi ba.

Allah ya sa mu dace, amin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dabbobin LayyaLayyaRago
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping: Sa Mutane A Matsayi Mafi Muhimmanci A Zuciya

Next Post

Jiragen Dakon Kaya Masu Zirga-zirga Tsakanin Sin Da Turai Sun Gudanar Da Zirga-zirga Mafi Yawa A Mayu

Related

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci
Addini

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

6 days ago
An Gano Cushen Biliyan 5 Cikin Kasafin Kuɗin Hukumar Alhazai Ta Ƙasa
Addini

An Gano Cushen Biliyan 5 Cikin Kasafin Kuɗin Hukumar Alhazai Ta Ƙasa

1 week ago
Nijeriya Za Ta Karɓi Bakuncin Gasar Karatun Alƙur’ani Mai Girma Ta Duniya
Addini

Nijeriya Za Ta Karɓi Bakuncin Gasar Karatun Alƙur’ani Mai Girma Ta Duniya

2 weeks ago
Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025
Addini

Gwamnan Legas Ya Nemi A Dakatar Da Marasa Lafiya Zuwa Aikin Hajjin 2025

1 month ago
Gwamnan Bauchi Ya Yi Alhanin Rasuwar Shaikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi 
Addini

Gwamnan Bauchi Ya Yi Alhanin Rasuwar Shaikh Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi 

1 month ago
Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu
Da ɗumi-ɗuminsa

Fitaccen Malamin Musulunci Mai Da’awar Sunnah A Nijeriya, Dr. Idris Dutsen Tanshi Ya Rasu

1 month ago
Next Post
Jiragen Dakon Kaya Masu Zirga-zirga Tsakanin Sin Da Turai Sun Gudanar Da Zirga-zirga Mafi Yawa A Mayu

Jiragen Dakon Kaya Masu Zirga-zirga Tsakanin Sin Da Turai Sun Gudanar Da Zirga-zirga Mafi Yawa A Mayu

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.