ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

by Idris Aliyu Daudawa and Sulaiman
5 months ago
NECO

Gwamnatin tarayya ta karyata labaran da ake ta yadawa ta kafar sadarwa ta zamani cewar gwamnatin tarayya ta soke jarrabwar WAEC da NECO wadanda aka yi a shekarar 2025 saboda abubuwan da aka yi wadanda suka sabawa dokokin jarabawar biyu.

A sanarwar da ma’aikatar ilimi ta tarayya ta fitar makon daya gabata wadda kuma dauke da sa hannun darekta na ‘yan jarida da hulda da jama’a, Boriowo Folasade, ya sake ya bayyana rahoton, a matsayin wani abu ne da aka shirya shi, domin a tada hankalin al’umma da suka hada da dalibai, Iyaye, da jama’a baki daya.

  • Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta
  • Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Ma’aikatar ta tabbatar da cewa an kammala jarabawar WAEC ta shekarar 2025 cikin nasara ba tare da wata matsala ba,in da an hadu da wasu matsaloli amma an yi maganinsu da hukumar ita ta yi hakan.

ADVERTISEMENT

Hakanan ma ta kara yin bayani cewar jarrabawar NECO da ana yin ta ba tare da wata matsala ba, a daidai lokacin da ake shi wannan jawabin babu wta matsalar da aka hadu da ita.

Ma’aikatar ta jaddada bata samu wani labara ba daga wani jami’inta ko rahoto daga hukumomin WAEC, da NECO ko kuma wata hukumar dangane da wani abinda aka yi daya sabwa doka lokacin jarrabawar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Haramta Karɓa Ko Sauyawa Ɗalibai Aji Kai Tsaye Zuwa SS3

Obi Ya Yi Alkawarin Biyan Kudin Jarrabawar NECO Na Fursunoni 148

Don haka nema tayi kira da jama’a kada suyi amfani da shi labarin daya zaman a kanzon kurege da ake ta yadawa,idan wani bayani suke bukata su tuntubi kafa da suka san ba zata yi zuki ta malle ba,ko kuma jami’an ma’aikatar ilimi ta kafar sadarwarsu ko kuma na, WAEC, da NECO.

“An ja hankalin ma’aikatar ilimi ta tarayya akan wani labara ko rahoton da ya karade kafafen sadarwa na zamani,inda aka yi maganar cewar ban soke jarabawar WAEC ta shekarar 2025 da aka yi saboda an samu laifin aikata magudi lokacin da ake yin ta.

“Ma’aikatar tace don haka tana sanar da jama’a cewa ta yi nesa da kanta,dangane da ita sanarwar ko labarin saboda kuwa ai na kanzon kurege ne inda ta kara jaddada: Jarabawar, WAEC ta shekarar 2025,an kammala ta cikin nasara ba tare da wata matsalar data gagara shawo kai ba,in banda wadansu ‘yan kananan laifukan da suka auku,wadanda kuma ita hukumar tayi maganinsu.

“Ita kuma jarabawar NECO ana yinta ba tare da wata matsala ba, ya zuwa kuma hali ko lokacin da ake ciki babu wata matsalar da aka fuskanta. Ma’aikatar ilimi ta tarayya bata samu wani sako ba a hukumance daga WAEC ko kuma NECO,ko kuma duk wata hukuma mai shirya jarabawa da ke nuna an samu aikata magudin jarabawa.”

Ma’aikatar har yanzu babu wani abinda daya tada mata hankali wanda ya wuce aikata lamurran da suka shafi jarabawa cikin gaskiya da rikon amana,da kuma kwanciyar hankali, tana aiki kafada da kafada da su hukumomin jarrabawar,domin a samu inganta yadda ake lura da sa idon dangane da yadda ake gudanar da jarabawar.

Daga karshe ma’aikatar ta kara jaddada ta sha alwashin yadda ake gudanar da jarabawar yayi daidai kamar yadda dokokin hukumar suka bayyana, na samun gaskiya kan duk wata jarabawar da ake yi a Nijeriya,don haka su hukumomin jarrabawar jarabawar abokan huldar ta ne da kuma aiki tare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Haramta Karɓa Ko Sauyawa Ɗalibai Aji Kai Tsaye Zuwa SS3
Ilimi

Gwamnatin Tarayya Ta Haramta Karɓa Ko Sauyawa Ɗalibai Aji Kai Tsaye Zuwa SS3

December 14, 2025
Obi Ya Yi Alkawarin Biyan Kudin Jarrabawar NECO Na Fursunoni 148
Ilimi

Obi Ya Yi Alkawarin Biyan Kudin Jarrabawar NECO Na Fursunoni 148

December 14, 2025
Fadar Shugaban Kasa Ta Karrama Daliban Da Suka Nuna Hazaka A 2025
Ilimi

Fadar Shugaban Kasa Ta Karrama Daliban Da Suka Nuna Hazaka A 2025

November 30, 2025
Next Post
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.