• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

by Sulaiman
2 days ago
in Labarai
0
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

GORON JUMA’A 01-07-2025

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

Rikicin da ya barke tsakanin Fulani da Gwarawa a kauyen Gurfata da ke karamar hukumar Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ya yi sanadin mutuwar mutum daya tare da raunata wasu da dama, yayin da wasu da dama suka rasa muhallansu bayan da aka kona gidaje 31.
Lamarin wanda ya afku a ranar Talatar da ta gabata, rahotanni sun ce ya samo asali ne daga takaddamar hanya da ta bi ta cikin gonar wani manomi gwari mai suna Sa’adu wacce wani Bafulatani makiyayi mai suna Shaibu Adamu ya yi yunkurin bi da shanunsa ta kan wannan hanya.
  • Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana
Mai sharhi kan harkokin tsaro, Zagazola Makama, ya bayar da cikakken rahoto game da rikicin a wani bayani da ya wallafa a shafinsa na X (Twitter) a ranar Laraba.
A cewar Makama, rikicin ya fara ne a lokacin da Adamu ya yi yunkurin ratsa gonar Sa’adu, amma manomin ya ki amincewa, inda ya dage sai dai ya bi ta wata hanya ta daban.
Makama ya ce rashin jituwar da ke tsakanin mutanen biyu ta kai ga doke-doke.
“Nan da nan, al’amura suka kara kazanta yayin da dan uwan makiyayi Shaibu, Adamu Ibrahim, ya kai wa wani manomi dan garin hari, Dahiru Yakubu, da adda.
“An garzaya da Yakubu zuwa Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abuja, inda daga baya ya rasu,” In ji Makama.
Labarin mutuwar Yakubu ya haifar da harin ramuwar gayya daga fusatattun matasan Gwari, inda suka far wa Fulani a kauyen, inda suka kona gidaje 31 tare da raunata akalla mutane uku.
Daga baya an tura sojoji tare da wasu jami’an tsaro zuwa yankin domin kwantar da tarzoma da kuma dawo da zaman lafiya.
“Hukumomi sun yi kira da a samar da zaman lafiya tare da yin kira ga al’ummomin biyu da su yi hakuri, a halin da ake ciki, ana ci gaba da kokarin sasanta bangarorin biyu da kuma hana barkewar rikici.”
Ya kara da cewa har zuwa yau Laraba al’amura sun koma kamar yadda aka saba duk da cewa har yanzu ana zaman dar-dar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Next Post

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Related

GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 01-07-2025

48 minutes ago
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano
Manyan Labarai

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

1 hour ago
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin
Manyan Labarai

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

4 hours ago
Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni
Labarai

Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

5 hours ago
Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul
Manyan Labarai

Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul

7 hours ago
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka
Labarai

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

15 hours ago
Next Post
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 01-07-2025

August 1, 2025
An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

An Zaɓi Saidu Yahya A Matsayin Shugaban Hukumar Yaƙi Da Cin Hanci Ta Kano

August 1, 2025
Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

August 1, 2025
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447 Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa

August 1, 2025
Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

Shekara 2 Ta Gwamnatin Tinubu: Gwamnonin Arewa Sun ƙaryata Zargin ACF Na Watsi ɗa Yankin

August 1, 2025
Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

August 1, 2025
Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

August 1, 2025
Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul

Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul

August 1, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

July 31, 2025
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.