• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

by Leadership Hausa
21 hours ago
in Siyasa
0
Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yanza haka sanatoci biyu kacal ya rage wa jamƴyar APC ta samu kashi biyu cikin uku na yawan ƴan majalisar dattawa, sakamakon sauya sheƙa da sanatoci guda huɗu suka yi daga PɗP zuwa APC a ranar Laraba da ta gabata.

Bisa tsarin kundin mulkin Nijeriya da dokokin majalisar ƙasa, wannan na nufin cewa idan APC ta samu kashi biyu bisa uku na yawan mambobi a majalisar dattawa, kowanne ƙudirin doka ko wata buƙata da aka kawo zauren majalisar dattawa dole sai ya samu goyon bayan APC kafin a amince da shi ko ba tare da goyon bayan ƴan adawar ba. 

Masana sharhi kan harkokin siyasa su yi gargaɗin cewa irin wannan rinjaye na haifar da babbar barazana ga dimokuraɗiyyar Nijeriya da ke tasowa kuma yana iya haifar da mulkin kama-karya.

  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Sake Ciyo Bashin Dala Biliyan 21 Daga Ƙetare
  • Wasu Gwamnonin PDP Sun Kulla Makirci Kan Samun Shugaban Kasa Daga Yankin Kudu —Wike

Sanatocin guda hudu da suka sauya sheƙa a makon da ya gabata sun kasance biyu daga Jihar Akwa Ibom da kuma daga Jihar Osun, sun bayyana ficewarsu a lokacin taron zaman majalisar. Sanatocin sun hada da Sanata Sampson Ekong, mai wakiltar Akwa Ibom ta kudu da Aniekan Bassey, mai wakiltar Akwa Ibom ta arewa maso gabas da Francis Fadahunsi, mai wakiltar Osun ta gabas da kuma Olubiyi Fadeyi, mai wakiltar Osun ta tsakiya.

Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya karanta wasiƙar sauya sheƙar a zauren majalisar.

Labarai Masu Nasaba

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

Saboda haka, ƙarfin APC a zauren majalisar dattawa mai mambobi 109 ya kai 70, kujeru biyu kadai take buƙata ta cika 72 don samun rinjaye na kashi biyu cikin uku.

PɗP yanzu haka tana da kujeru 28, yayin da jam’iyyar LP ke da biyar. Jam’iyyar SɗP na da kujeru biyu, yayin da jam’iyyar NNPP da APGA ke da kujeru guda daya kowannansu.

A yanzu haka, akwai kujeru biyu na majalisar dattawa da babu kowa. Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), har yanzu ba ta gudanar da zaɓen cire gurbin Sanata Ifeanyi Ubah, mai wakiltar Anambra ta kudu, wanda ya rasu a farkon wannan shekara, da Sanata Monday Okpebholo, mai wakiltar Edo ta tsakiyar, wanda ya bar kujerarsa bayan lashe zaɓen gwamna na Jihar Edo a 2024.

Kazalika, a majalisar wakilai ma an samu sauya sheƙar mambobi guda uku daga PɗP zuwa APC a ranar Laraba, wanda ya kuma ƙara ƙarfafa ƙarfin jam’iya mai mulki zuwa samun kujeru 224 a cikin kujeru 360 na majalisar. ƴan majalisar wakilan da suka saura sheƙa sun hada da Taofeek Ajilesoro da Omirin Emmanuel Olusanya daga Jihar Osun, tare da Marcus Onobun daga Jihar Edo da kuma Mark Esset daga Akwa Ibom.

Bisa wannan lamari, PɗP yanzu tana da kujeru 86, yayin da jam’iyyar LP take da kujeru 26, NNPP ta da 16, APGA ta da shida, SɗP ta da biyu, sannan ADC tana da daya.

A halin yanzu, akwai kujeru biyar a majalisar wakilai da babu kowa sakamakon mutuwar ƴan majalisar guda huɗu da kuma daya da ya yi murabus.

da yake tsokaci kan samun rinjayen APC a zauren a majalisun tarayya a gaban zabɓen 2027, masana kimiyyar siyasa, Farfesa Gbade Ojo, ya yi gargaɗi game da mummunan sakamako ga makomar dimokuraɗiyyar Nijeriya.

Ya ce, “Abin da muke shaida shi ne, APC na ƙara samun gagarumin rinjaye. ɗuk da cewa hakan na iya bayyana matsayin siyasa mai ƙarfi a zahiri, tasirin wannan ga dimokuraɗiyya yana da matukar damuwa. 

“Lokacin da wata jam’iyyar mai mulki a cikin dimokuraɗiyya ta mamaye majalisa har ta samu kashi biyu cikin uku na yawan mambobi, hakan yana zama wani siffofi na mulkin kama-kurya, domin ba za a samu ingantaccen kulawa da daidaito ba,” in ji shi.

Ya ba da shawara cewa a irin wannan yanayi, majalisun tarayya na iya rasa ƴancin kai da zama ƴan amshin shata ga ɓangaren zantarwa.

Ya gargaɗin cewa in har ƴan adwa ba su sake tsarawa ba ta hanyar dawo da tsaftataccen tsarin cikin gida da kafa wani takamaiman aƙidar tunani, dimokuraɗiyyar Nijeriya za ta ci gaba da kasancewa cikin hatsari da rashin daidaito.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCDimokuraɗiyyamajalisaSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

Next Post

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Related

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12
Siyasa

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

12 hours ago
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
Siyasa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2 days ago
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili
Siyasa

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

2 days ago
Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
Siyasa

Tinubu Ya Cika Alƙawurran Da Ya Ɗauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

2 days ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Labarai

2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC

3 days ago
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa
Siyasa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

4 days ago
Next Post
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.