ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

by Leadership Hausa
12 months ago
APC

A yanza haka sanatoci biyu kacal ya rage wa jamƴyar APC ta samu kashi biyu cikin uku na yawan ƴan majalisar dattawa, sakamakon sauya sheƙa da sanatoci guda huɗu suka yi daga PɗP zuwa APC a ranar Laraba da ta gabata.

Bisa tsarin kundin mulkin Nijeriya da dokokin majalisar ƙasa, wannan na nufin cewa idan APC ta samu kashi biyu bisa uku na yawan mambobi a majalisar dattawa, kowanne ƙudirin doka ko wata buƙata da aka kawo zauren majalisar dattawa dole sai ya samu goyon bayan APC kafin a amince da shi ko ba tare da goyon bayan ƴan adawar ba. 

Masana sharhi kan harkokin siyasa su yi gargaɗin cewa irin wannan rinjaye na haifar da babbar barazana ga dimokuraɗiyyar Nijeriya da ke tasowa kuma yana iya haifar da mulkin kama-karya.

ADVERTISEMENT
  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Sake Ciyo Bashin Dala Biliyan 21 Daga Ƙetare
  • Wasu Gwamnonin PDP Sun Kulla Makirci Kan Samun Shugaban Kasa Daga Yankin Kudu —Wike

Sanatocin guda hudu da suka sauya sheƙa a makon da ya gabata sun kasance biyu daga Jihar Akwa Ibom da kuma daga Jihar Osun, sun bayyana ficewarsu a lokacin taron zaman majalisar. Sanatocin sun hada da Sanata Sampson Ekong, mai wakiltar Akwa Ibom ta kudu da Aniekan Bassey, mai wakiltar Akwa Ibom ta arewa maso gabas da Francis Fadahunsi, mai wakiltar Osun ta gabas da kuma Olubiyi Fadeyi, mai wakiltar Osun ta tsakiya.

Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya karanta wasiƙar sauya sheƙar a zauren majalisar.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Saboda haka, ƙarfin APC a zauren majalisar dattawa mai mambobi 109 ya kai 70, kujeru biyu kadai take buƙata ta cika 72 don samun rinjaye na kashi biyu cikin uku.

PɗP yanzu haka tana da kujeru 28, yayin da jam’iyyar LP ke da biyar. Jam’iyyar SɗP na da kujeru biyu, yayin da jam’iyyar NNPP da APGA ke da kujeru guda daya kowannansu.

A yanzu haka, akwai kujeru biyu na majalisar dattawa da babu kowa. Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), har yanzu ba ta gudanar da zaɓen cire gurbin Sanata Ifeanyi Ubah, mai wakiltar Anambra ta kudu, wanda ya rasu a farkon wannan shekara, da Sanata Monday Okpebholo, mai wakiltar Edo ta tsakiyar, wanda ya bar kujerarsa bayan lashe zaɓen gwamna na Jihar Edo a 2024.

Kazalika, a majalisar wakilai ma an samu sauya sheƙar mambobi guda uku daga PɗP zuwa APC a ranar Laraba, wanda ya kuma ƙara ƙarfafa ƙarfin jam’iya mai mulki zuwa samun kujeru 224 a cikin kujeru 360 na majalisar. ƴan majalisar wakilan da suka saura sheƙa sun hada da Taofeek Ajilesoro da Omirin Emmanuel Olusanya daga Jihar Osun, tare da Marcus Onobun daga Jihar Edo da kuma Mark Esset daga Akwa Ibom.

Bisa wannan lamari, PɗP yanzu tana da kujeru 86, yayin da jam’iyyar LP take da kujeru 26, NNPP ta da 16, APGA ta da shida, SɗP ta da biyu, sannan ADC tana da daya.

A halin yanzu, akwai kujeru biyar a majalisar wakilai da babu kowa sakamakon mutuwar ƴan majalisar guda huɗu da kuma daya da ya yi murabus.

da yake tsokaci kan samun rinjayen APC a zauren a majalisun tarayya a gaban zabɓen 2027, masana kimiyyar siyasa, Farfesa Gbade Ojo, ya yi gargaɗi game da mummunan sakamako ga makomar dimokuraɗiyyar Nijeriya.

Ya ce, “Abin da muke shaida shi ne, APC na ƙara samun gagarumin rinjaye. ɗuk da cewa hakan na iya bayyana matsayin siyasa mai ƙarfi a zahiri, tasirin wannan ga dimokuraɗiyya yana da matukar damuwa. 

“Lokacin da wata jam’iyyar mai mulki a cikin dimokuraɗiyya ta mamaye majalisa har ta samu kashi biyu cikin uku na yawan mambobi, hakan yana zama wani siffofi na mulkin kama-kurya, domin ba za a samu ingantaccen kulawa da daidaito ba,” in ji shi.

Ya ba da shawara cewa a irin wannan yanayi, majalisun tarayya na iya rasa ƴancin kai da zama ƴan amshin shata ga ɓangaren zantarwa.

Ya gargaɗin cewa in har ƴan adwa ba su sake tsarawa ba ta hanyar dawo da tsaftataccen tsarin cikin gida da kafa wani takamaiman aƙidar tunani, dimokuraɗiyyar Nijeriya za ta ci gaba da kasancewa cikin hatsari da rashin daidaito.

APC
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Next Post
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

LABARAI MASU NASABA

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

Cikakken Jerin Yan Wasan Da Suka Lashe Kyautuka A Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

Sojoji Sun Kama Wani Ɗan Sudan Da Ake Zargi Da Haɗa Kai Da ’Yan Ta’adda A Borno

July 20, 2026
Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

Matashi Ya Mutu, Wasu Da Dama Sun Jikkata Yayin Murnar Lashe Kofin Duniya Da Spain Ta Yi

July 20, 2026
Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

Mbappé Ya Zama Mafi Yawan Ƙwallaye A Tarihin Gasar Kofin Duniya

July 20, 2026
An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

An Yi Babban Taro Kan Tsarin Shugabancin Duniya A Bangaren AI A Shanghai

July 20, 2026
Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

July 19, 2026
Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

July 19, 2026
Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

Dalibai 4 Da Ke Wakiltar Kasar Sin A Gasar Kasa Da Kasa Ta Chemistry Olympiad Sun Lashe Lambobin Zinare

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.